Aminiya:
2025-07-07@06:40:36 GMT

Gwamnatin Kano ta ƙaddamar da rabon abincin buɗa-baki

Published: 3rd, March 2025 GMT

Gwamnatin Kano ta ƙaddamar da rabon abincin buɗa-baki domin tallafa wa mabuƙata a wannan wata mai albarka na Ramadana.

Mataimakin Gwamnan Kano, Kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo ne ya ƙaddamar da rabon abincin a cibiyar Dandali da ke Ƙaramar Hukumar Fagge a jihar.

HOTUNA: Tinubu ya karɓi baƙuncin Shugaban Saliyo a Abuja NLC ta yi fatali da yunƙurin ƙara kuɗin lantarki

Bayanai sun ce gwamnatin jam’iyyar NNPP ƙarƙashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf da ta ƙaddamar da wannan shiri tana da burin raba abincin buɗa-baki ga mabuƙata masu azumtar watan Ramadana.

Gwamnatin ta ce an tanadi cibiyoyi 91 domin raba wa mabuƙata 91,000 abincin buɗa-baki duk rana nan da tsawon kwanaki 27 masu zuwa.

Domin tabbatar da samun nasara, gwamnatin ta ce ta ɗauki masu aikin girke-girke da za su riƙa dafawa sannan su raba wa mabuƙata abincin.

Mataimakin Gwamnan wanda shi ne ke jagorantar shirin raba abincin a bana, ya bayyana gamsuwarsa da yadda aka ƙaddamar da shirin, yana mai kiran waɗanda aka ɗora wa alhakin aikin su tabbatar da raba wa mabuƙata abincin a kan kari.

Aminiya ta ruwaito cewa, Mataimakin Gwamnan ya samu rakiyar wasu ƙusoshin Gwamnatin Kano wajen ƙaddamar da rabon abincin da suka haɗa da Kwamishinan Labarai da Harkokin Cikin Gida, Ibrahim Abdullahi Waiya da Kwamishinan Harkokin Addini, Sheikh Tijjani Auwal da sauransu.

Gwamnatin Kano ta jaddada ƙudirinta na rage raɗaɗin al’umma musamman Musulmi a wannan wata mai falala.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Aminu Abdussalam Gwarzo Buɗa baki Jihar Kano Ramadan ƙaddamar da rabon abincin abincin buɗa baki Gwamnatin Kano wa mabuƙata

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna ya gargaɗi sarakuna kan mamaye filayen kiwo a Gombe

Gwamnan Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya gargaɗi sarakunan gargajiya a faɗin ƙananan hukumomi 11 na jihar kan zargin hannu a mamaye hanyoyin kiwo da filayen kiwo, abin da ke haddasa rikici tsakanin makiyaya da manoma.

Gwamnan ya nuna damuwa kan rahotannin da ke cewa wasu sarakuna na karɓar cin hanci suna kuma ba da damar shiga filayen kiwo ba bisa ƙa’ida ba, lamarin da ke ƙara tayar da zaune tsaye a tsakanin al’umma.

Majalisar Dattawa ta gindaya sharaɗin dawo da Sanata Natasha Ambaliyar ruwa ta yi ajalin mutum 50 a Amurka

“Duk wanda aka kama yana da hannu a wannan aika-aikar, za mu hukunta shi bisa doka,” in ji Gwamna.

Ya kuma roƙi makiyaya da su guji shiga gonaki domin hakan na haifar da rikici maras amfani.

Ya jaddada cewa gwamnatinsa za ta aiwatar da shawarwarin kwamitin da ke bincike kan lamarin, tare da tabbatar da zaman lafiya mai ɗorewa ta hanyar kare hanyoyin kiwo da tabbatar da adalci wajen amfani da filaye.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Turji: Sai ka sako mutanen da ka sace za a yi sulhu — Gwamnatin Sakkwato
  • Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya
  • Gwamna ya gargaɗi sarakuna kan mamaye filayen kiwo a Gombe
  • Tsadar rayuwa ta sa ’yan Nijeriya na siyan abincin da ya lalace
  • Kasar Iran Ta Jaddada Wajabcin Hukunta Gwamnatin Mamayar Isra’ila Dangane Da  Ta’addancinta Kan Iran
  • Kungiyar Hamas Ta Sanar Da Matsayinta Kan Shirin Dakatar Da Bude Tsakaninta Da Gwamnatin Mamayar Isra’ila
  • Hadiman gwamnan Kano sun haura 300 bayan naɗa wasu sabbi 19
  • Gwamnan Bauchi ya ƙaddamar da kwamitin ƙirƙiro da sabbin masarautu
  • Amurka Ta Kakabawa JMI Sabbin Takunkuman Tattalin A Jiya Alhamis
  • Makusantan Gwamnatin Buhari da suka shiga haɗakar ADC