Gwamnatin Yamen Ta Gargadi HKI Da Amurka Kan Cewa Tana Sa Ido A Kan Abinda Ke Faruwa Da Tsagaita Wuta A Gaza
Published: 3rd, March 2025 GMT
Kungiyar Ansarallah ta kasar Yemen ta gargadi HKI da kuma Amurka kan cewa, tana sanya ido a kan yadda suke sabawa yarjeniyar budewa juna wuta da suka cimma da su. Musamman yadda HKI ta sabawa yarjeniyar a mashigar Rafah na barin abinci ya shiga Gaza, da kuma bukatar sake tattauna wasu al-amura a yarjeniyar.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran nakalto Hazem Al-asad mamba a majalisar siyasa ta kasar Yemen, yana fadar haka, ya kuma kara da cewa, kungiyar a shirye take ta sake shiga yaki da Amurka, a duk lokacinda suka yi kokarin cutar da mutanen Gaza.
Al-Asad ya gargadi gwamnatin Amurka da masu goyon bayan HKI a duk wata cutarwa da zata yiwa mutanen Gaza.
Har’ila yau, wani mamba a majalisar, Nasir-Addeen Amir ya bayyana cewa idanummu na kan abubuwan da suke faruwa a Gaza, sannan hannayenmu suna kan na’urorin bude wuta a kan dukkan abubuwan da suka shafi HKI da Amurka, don kare mutanen Gaza.
Amir ya kara da cewa dukkan makamai masu linzami na kasar Yemen su na cikin shirin komawa yaki idan HKI ko kawayenta suka sake farwa mutanen gaza.
Ya kuma kammala da cewa mayakan ansarullah za su sake budewa jiragen ruwa masu zuwa HKI wuta a tekun maliya da sauran wuraren da ta kaiwa hare-hare a baya bayan an fara yakin Octoban shekara ta 2023.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Najeriya Ta Yi Allawadai Da Harin Da “Isra’ila” Ta Kawo Wa Iran
A wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen Najeriya ta fitar, ta yi tir da harin na Isra’ila akan Iran tare da bayyana cewa, ya haifar da rikici a tsakanin bangarorin biyu da kuma musayar harba makamai masu linzami.
Gwamnatin ta Najeriya ta nuna bakin cikinta akan abinda ya faru, tare da kuma da yin kiran a tsagaita wutar yaki da gaggawa, da kai zuciya nesa.
Har ila yau, sanarwar ma’aikatar harkokin wajen ta Nigeria wacce kakakinta Kimiebi Imomotimi Ebienfa ya rattabawa hannu a yau Asabar,14 ga watan Yuni 2025, ta jaddada cewa; yaki ba zai maye gurbin tattaunawa ba, kuma hanyar diplomasiyya ce za ta kai ga samar da zaman lafiya mai dorewa, girmama juna da aiki da dokokin kasa da kasa.,