Gwamnatin Yamen Ta Gargadi HKI Da Amurka Kan Cewa Tana Sa Ido A Kan Abinda Ke Faruwa Da Tsagaita Wuta A Gaza
Published: 3rd, March 2025 GMT
Kungiyar Ansarallah ta kasar Yemen ta gargadi HKI da kuma Amurka kan cewa, tana sanya ido a kan yadda suke sabawa yarjeniyar budewa juna wuta da suka cimma da su. Musamman yadda HKI ta sabawa yarjeniyar a mashigar Rafah na barin abinci ya shiga Gaza, da kuma bukatar sake tattauna wasu al-amura a yarjeniyar.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran nakalto Hazem Al-asad mamba a majalisar siyasa ta kasar Yemen, yana fadar haka, ya kuma kara da cewa, kungiyar a shirye take ta sake shiga yaki da Amurka, a duk lokacinda suka yi kokarin cutar da mutanen Gaza.
Al-Asad ya gargadi gwamnatin Amurka da masu goyon bayan HKI a duk wata cutarwa da zata yiwa mutanen Gaza.
Har’ila yau, wani mamba a majalisar, Nasir-Addeen Amir ya bayyana cewa idanummu na kan abubuwan da suke faruwa a Gaza, sannan hannayenmu suna kan na’urorin bude wuta a kan dukkan abubuwan da suka shafi HKI da Amurka, don kare mutanen Gaza.
Amir ya kara da cewa dukkan makamai masu linzami na kasar Yemen su na cikin shirin komawa yaki idan HKI ko kawayenta suka sake farwa mutanen gaza.
Ya kuma kammala da cewa mayakan ansarullah za su sake budewa jiragen ruwa masu zuwa HKI wuta a tekun maliya da sauran wuraren da ta kaiwa hare-hare a baya bayan an fara yakin Octoban shekara ta 2023.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Fira Ministan Spain: Bai Kamata A Rika Barin “Isr’ila” Tana Shiga Gasar
Wasannin Duniya Ba
Fira ministan kasar ta Spain ya bayyana hakan ne dai a yayin da yake nuna jin dadinsa danagen da gagarumar Muzaharar da mutanen kasar su ka yi ta nuna kin amincewarsu da shigar kasar ta Yahudawa cikin tseren kekune.
Fira ministan kasar ta Spain Pedro Sánchez Pérez ya ce: ” Har zuwa lokacin da za a kawo karshen kisan kiyashi a Gaza, bai kamata a kyale Isra’ila ta rika shiga cikin gasar wasannin kasa da kas aba.
A yau litinin ne dai Fira ministan kasar ta Spain ya gabatar da jawabi gabanin taron ‘yan majalisa masu wakiltar jam’iyyun gurguzu, ya yi ishara da taho mu gamar da aka yi a tsakanin masu kin jinin kisan kiyashin da HKI take yi wa Falasdinawa da masu goyon bayanta, sannan ya kara da cewa; a kodayaushe ba mu aminta da tashin hankali ba.
Mutane 20 ne dai su ka jikkata a yayin wannan taho mu gama din a babban birnin kasar ta Spain,Madrid.
Fira ministan Pedro Sánchez Pérez ya kuma yi wa hukumomin wasanni na duniya tamabya da cewa; Me ya sa aka haramtawa Rasha shiga cikin wasannin kasa da kasa saboda yakin Ukiraniya,amma ba a kori Isra’ila ba?.
Al’ummar kasar Spain da mahukuntanta suna cikin nag aba-gaba a cikin nahiyar turai wajen nuna kin amincewa da yi wa mutanen Gaza kisan kiyashi.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Shugaban Kasar Iran Ya Gana Da Sarkin Kasar Qatar A Birnin Doha September 15, 2025 Dan Kasar Iran Mai Kirkira Ya Sami Kyautar Yabo A Kasar China September 15, 2025 Fizishkiyan: Wajibi Ne Musulmi Su Hada Kai Domin Dakatar Da Laifukan HKI September 15, 2025 Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Qatar, Turkiyya, Pakistan Da Labanon A Doha September 15, 2025 Kwamitin Kolin Tsron Kasar Iran Ya Amince Da Yarjejeniyar Da Aka Cimma Da Hukumar IAEA September 15, 2025 Jami’in Kasar Yemen Ya Aike Da Sako Ga Mahalarta Taron Birnin Doha Na Kasar Qatar September 15, 2025 Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sakamakon Kisan Kiyashin ‘Yan Sahayoniyya A Gaza Ya Kusaci 65,000 September 15, 2025 Gwamnatin Sudan Ta Ce: Babu Sulhu Da ‘Yan Tawayen Kasar Na Kungiyar Rapid Support Forces September 15, 2025 Kasashen Larabawa da na Musulmi na taron gaggawa kan harin Isra’ila a Qatar September 15, 2025 Hamas ta bukaci kasashen musulmi da na Larabawa su dauki mataki mai tsari kan Isra’ila September 15, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci