Gwamnatin Jihar Kano Ta Kaddamar Da Shirin Ciyarwar Na Watan Ramadan
Published: 3rd, March 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Kano ta kaddamar da shirin ciyarwa a watan Ramadan na shekarar 2025 a hukumance, da nufin samar da abincin buda baki ga mabukata 91,000 a fadin jihar.
Shirin wanda zai dauki tsawon kwanaki 27 yana daga cikin kokarin da gwamnatin jihar ke yi na tallafawa dimbin al’ummarta a watan na Ramadan.
Mataimakin gwamnan jihar Kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo wanda kuma shi ne shugaban shirin, ya kaddamar da shirin a hukumance a cibiyar Dandali dake karamar hukumar Fagge.
Ya nuna jin dadinsa da yadda aka gudanar da shirin cikin kwanciyar hankali, tare da yin kira ga kamfanonin da abin ya shafa da su tabbatar da isar da abinci cikin lokaci da inganci a dukkanin cibiyoyin ciyar da abincin.
Za a aiwatar da shirin a cibiyoyin ciyar da abinci 91 da aka keɓe, inda aka tanadar da masu dafa abinci don ciyar da mutum 91,000 abinci a kowace rana.
Gwamnatin jihar Kano ta ware makudan kudade domin tabbatar da nasarar shirin, inda ta nuna aniyar ta na tallafawa marasa galihu a wannan wata na Ramadan.
Bikin kaddamar da shirin ya samu halartar manyan jami’an gwamnati da suka hada da kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya, da kwamishinan harkokin addini, Sheikh Tijjani Auwal.
Daga Khadija Aliyu
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Ramadan
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai
A jawabinsa yayin taron, Gwamna Sani ya gabatar da kasida mai taken: “Gina Haɗin Gwiwa Domin Ci Gaban Kowa”, inda ya bayyana yadda Jihar Kaduna ke ci gaba da samun nasara a fannoni da dama kamar gyaran birane, bunƙasa noma, da tsarin tallafiwa jama’a.
Gwamnan Ya ce tsarin ci gaban jihar yana dogara ne kan faɗaɗa damar tattalin arziki da kare marasa ƙarfi, da ƙarfafa jama’a su samu nasara a rayuwarsu.
Gwamna Uba Sani, ya kuma halarci shirin baje koli na birnin Dubai mai taken : “Sauya Arewa a Nijeriya: Jagoranci, Ƙirƙira, da Tasirin Zamantakewa”, inda nan ma ya jaddada cewa jagoranci mai nagarta da amfani da fasaha a mulki suna da matuƙar muhimmanci wajen buɗe damarmaki ga mutane da birane.
A yayin taron, Gwamnan ya gudanar da wata ganawa ta musamman da Marwan Bin Galita, Darakta Janar na birnin Dubai inda suka tattauna batutuwan haɗin gwiwa a fannin kirkirar makamashin sharar gida da kula da sharar gida ta zamani, da kuma tsare-tsaren gine-ginen birane na zamani.
A ganawar, duk Bangarorin biyu sun amince da zurfafa haɗin kai a fannin fasaha da musayar ƙwarewa domin tallafawa sauyin jihar Kaduna zuwa tattalin arzikin mai ɗorewa.
Gwamna Sani ya bayyana cewa halartar Jihar Kaduna a taron (APCS 2025) na nuna shirin jihar na shiga sahun ƙasashen duniya wajen yin haɗin kai, ƙirƙira, da zama abin koyi a fannin ci gaba mai ɗorewa da ci gaban kowa da kowa a fadin Nijeriya da ma duniya baki ɗaya
ShareTweetSendShare MASU ALAKA