Gwamnatin Jihar Kano Ta Kaddamar Da Shirin Ciyarwar Na Watan Ramadan
Published: 3rd, March 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Kano ta kaddamar da shirin ciyarwa a watan Ramadan na shekarar 2025 a hukumance, da nufin samar da abincin buda baki ga mabukata 91,000 a fadin jihar.
Shirin wanda zai dauki tsawon kwanaki 27 yana daga cikin kokarin da gwamnatin jihar ke yi na tallafawa dimbin al’ummarta a watan na Ramadan.
Mataimakin gwamnan jihar Kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo wanda kuma shi ne shugaban shirin, ya kaddamar da shirin a hukumance a cibiyar Dandali dake karamar hukumar Fagge.
Ya nuna jin dadinsa da yadda aka gudanar da shirin cikin kwanciyar hankali, tare da yin kira ga kamfanonin da abin ya shafa da su tabbatar da isar da abinci cikin lokaci da inganci a dukkanin cibiyoyin ciyar da abincin.
Za a aiwatar da shirin a cibiyoyin ciyar da abinci 91 da aka keɓe, inda aka tanadar da masu dafa abinci don ciyar da mutum 91,000 abinci a kowace rana.
Gwamnatin jihar Kano ta ware makudan kudade domin tabbatar da nasarar shirin, inda ta nuna aniyar ta na tallafawa marasa galihu a wannan wata na Ramadan.
Bikin kaddamar da shirin ya samu halartar manyan jami’an gwamnati da suka hada da kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya, da kwamishinan harkokin addini, Sheikh Tijjani Auwal.
Daga Khadija Aliyu
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Ramadan
এছাড়াও পড়ুন:
Za A Watsa Shirin “Bayanan Magabata Dake Jan Hankalin Xi Jinping” A Kafofin Watsa Shirye-shiryen Kasashen Tsakiyar Asiya Biyar
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp