Aminiya:
2025-05-01@03:38:38 GMT

Ɓacewar bindigogi 4,000: Sakaci ne dalili —’Yan sanda

Published: 3rd, March 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sandan Najeriya ta ɗora laifin ɓacewar bindigo 3,907 a hannun jami’anta a kan sakaci da kuma ƙarancin iliminsu game da kula da makamai.

Da take ƙarin bayani kan yawaitar ɓacewar bindigon, rundunar ta ɗora laifin ci gaban matsalar a kan abin da ta kira “sakacin” manyan jami’ai wajen tura ’yan sandan da ba su san ciwon kansu ba wajen aiki.

Rundunar ta bayyana takaicinta ne a wata takardar cikin gida daga “TERROFOR ABUJA” wanda wakilinmu ya yi katarin samu a ranar Lahadi.

Takardar ta fito a yayin da Majalisar Dattawa take gudanar da bincike kan rahoton Babban Mai Binciken Kudi na Tarayya da ya nuna manyan bindigon ’yan sanda 3,907 sun ɓace.

A kan haka ne Kwamitin Majalisar mai kula da Kayan Gwamnati ya yi wa Shugaban ’Yan Sandan Najeriya, Kayode Egbetekun da Mataimakin Sufeto-Janar mai Kula da Kuɗaɗe, Kasafi da Kayan Gwmanati, Suleiman Abdul, tambayoyin titsiye a kan ɓacewar bindigon.

Daga bisani kakakin rundunar, ACP Olumuyiwa Adejobi, ya fito ya bayyana cewa ɓata-gari ne suka yi awon gaba da bindigogin da ake magana a kai.

Ya kuma yi zargin cewa akwai aringizo a adadin da rahoton Babban Mai Binciken Kuɗin ya bayar na bindigogin da suka ɓace.

Sai dai kuma a wani saƙon cikin gida da Rundunar ta aika mai lamba CQ: 2400/DOPS/ CTU/FHQ/ABJ/VOL. 10/90, zuwa wa rassanta, ta gargaɗi manyan jami’anta cewa za su yaba wa aya zaƙi idan suka sake irin haka ta ƙara faruwa a ƙarƙashin jagorancinsu.

Saƙon ya kuma umarci manyan jami’an rundunar da su riƙa bayar da rahoton duk makaman da ke ƙarƙashin kulawarsu kafin ko a ranar 23 na kowane wata.

Rundunar ta aike saƙon ne ga sassauta da ke Kano da Maiduguri da Legas da Fatakwal da Abuja da Aba da Warri da Damaturu, ta gargaɗi manyan jami’anta cewa za su yaba wa aya zaƙi idan suka sake irin haka ta ƙara faruwa a ƙarƙashin jagorancinsu.

Sauran su e: Bauchi, Enugu, Jos, Minna, Kano, Yola, Ibadan, Owerii Makurdi, Lokoja, Gusau, Gombe, Lafia, Ilorin, Yenagoa, Uyo, Okija, Kaduna da Uburu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda manyan jami Rundunar ta

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnan Sokoto Ya Amince Da Sauya Wa Manyan Sakatarori 25 Ma’aikatu A Jihar 

Gwamnatin jihar ta ce, matakin na daya daga cikin kokarin gwamnati mai ci na inganta ayyukanta domin samar da romon dimokuraɗiyya ga al’ummar jihar Sokoto.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnan Sokoto Ya Amince Da Sauya Wa Manyan Sakatarori 25 Ma’aikatu A Jihar 
  • Tsoffin ma’aikatan NECO na neman a biya su bashin haƙƙoƙinsu
  • Ma’aikatar Sharia A Nan Iran Zata Bayyana Abinda ya farsu A Tashar Jiragen Ruwa Na Shahid Rajae
  • Dalilin da manyan ’yan siyasa ke barin NNPP — APC
  •  Manyan Malaman Roman Katolika Sun Fara Taron Zabar Paparoma
  •  Bom Da Ya Tashi A Arewa Maso Gabashin Najeriya Ya Kashe Mutane 6
  • Sabbin Bayanai Kan Fashe-Fashe Wasu Abubuwa A Tashar Jiragen Ruwan Kasar Iran
  • Gwamnatin Yobe Na Ƙoƙarin Inganta Tsaro – Hon. Idi Gubana
  • Shugaban Kungiyar Hizbullah Ya Abbaci Abubuwa 3 Wadanda Yakamata Kasar Ta Maida Hankali A Kansu
  • Tawagar Jami’ai Da ‘Yan Kasuwar Ta Tunusiya Ta Gana Da Mataimakin Shugaban kasar Iran