Aminiya:
2025-11-02@06:24:53 GMT

Ɓacewar bindigogi 4,000: Sakaci ne dalili —’Yan sanda

Published: 3rd, March 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sandan Najeriya ta ɗora laifin ɓacewar bindigo 3,907 a hannun jami’anta a kan sakaci da kuma ƙarancin iliminsu game da kula da makamai.

Da take ƙarin bayani kan yawaitar ɓacewar bindigon, rundunar ta ɗora laifin ci gaban matsalar a kan abin da ta kira “sakacin” manyan jami’ai wajen tura ’yan sandan da ba su san ciwon kansu ba wajen aiki.

Rundunar ta bayyana takaicinta ne a wata takardar cikin gida daga “TERROFOR ABUJA” wanda wakilinmu ya yi katarin samu a ranar Lahadi.

Takardar ta fito a yayin da Majalisar Dattawa take gudanar da bincike kan rahoton Babban Mai Binciken Kudi na Tarayya da ya nuna manyan bindigon ’yan sanda 3,907 sun ɓace.

A kan haka ne Kwamitin Majalisar mai kula da Kayan Gwamnati ya yi wa Shugaban ’Yan Sandan Najeriya, Kayode Egbetekun da Mataimakin Sufeto-Janar mai Kula da Kuɗaɗe, Kasafi da Kayan Gwmanati, Suleiman Abdul, tambayoyin titsiye a kan ɓacewar bindigon.

Daga bisani kakakin rundunar, ACP Olumuyiwa Adejobi, ya fito ya bayyana cewa ɓata-gari ne suka yi awon gaba da bindigogin da ake magana a kai.

Ya kuma yi zargin cewa akwai aringizo a adadin da rahoton Babban Mai Binciken Kuɗin ya bayar na bindigogin da suka ɓace.

Sai dai kuma a wani saƙon cikin gida da Rundunar ta aika mai lamba CQ: 2400/DOPS/ CTU/FHQ/ABJ/VOL. 10/90, zuwa wa rassanta, ta gargaɗi manyan jami’anta cewa za su yaba wa aya zaƙi idan suka sake irin haka ta ƙara faruwa a ƙarƙashin jagorancinsu.

Saƙon ya kuma umarci manyan jami’an rundunar da su riƙa bayar da rahoton duk makaman da ke ƙarƙashin kulawarsu kafin ko a ranar 23 na kowane wata.

Rundunar ta aike saƙon ne ga sassauta da ke Kano da Maiduguri da Legas da Fatakwal da Abuja da Aba da Warri da Damaturu, ta gargaɗi manyan jami’anta cewa za su yaba wa aya zaƙi idan suka sake irin haka ta ƙara faruwa a ƙarƙashin jagorancinsu.

Sauran su e: Bauchi, Enugu, Jos, Minna, Kano, Yola, Ibadan, Owerii Makurdi, Lokoja, Gusau, Gombe, Lafia, Ilorin, Yenagoa, Uyo, Okija, Kaduna da Uburu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda manyan jami Rundunar ta

এছাড়াও পড়ুন:

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

 

Da yake sharhi game da wannan batu a wani rubutu da ya yi a Facebook a ranar Alhamis, Sheikh Gumi ya ce, Sanda ta yi matukar nadama kuma ya tabbata ba halinta ba ne irin wannan mugun aiki face aikin shaiɗan ne ya yi sanadiyyar iftila’in, ba don son ranta ba ne.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC October 30, 2025 Manyan Labarai Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai October 30, 2025 Manyan Labarai Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar October 30, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
  • Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
  • Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Rundunar Sojin Nijeriya Ta Shirya Wa Janar Musa Faretin Gama Aiki
  • An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m
  • Matsalar Talauci Da Rashin Tsawon Rai Da ‘Yan Nijeriya Ke Fuskanta
  • Matsalar Tsaro: Ko Sabbin Shugabannin Rundunar Soji Za Su Kawo Sauyi?
  • Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 
  • Gobara ta tashi a babban kanti a Abuja