Aminiya:
2025-09-18@03:41:28 GMT

Abubuwan da ya kamata a sani game da azumin watan Ramadana

Published: 2nd, March 2025 GMT

Bismillahir Rahmanir Rahim Dukkan godiya ta tabbata ga Allah Wanda Ya isar da komai.

Tsira da amincin Allah su tabbata bisa ga Annabi (S.A.W) da kuma bayinsa zababbu.

Bayan haka. Wannan wani dan takaitaccen sako ne nake so na isar da shi ga ’yan uwa Musulmi, na ciro hujjojinta daga littafin Allah (S.

W.T) da kuma sunnar Manzo (S.A.W) da kuma zantukan maluma magabata da magada.

Sai na ambaci sunan littafin: “RAMADANIYYA” Ina ba da kyauta ga kowane Musulmi da Musulma wato mai Azumi, maza da mata.

Ina rokon Allah Ya sanya shi a cikin mizanin kyawawan ayyukanmu a ranar saduwa da Shi da Aljannar ni’ima. Allah Ya sa haka.

Ina rokon duk wanda ya ga wadansu kurakurai ya aikomin don nan gaba in gyara su. .

1. Ayoyi da suka yi magana a kan azumi

Da sunan Allah, mai Rahma, mai Jinkai. Allah Ya ce a cikin Al-Kur’ani Mai Girma: “Ya ku wadanda ku ka yi imani! An wajabta Azumi a kanku kamar yadda aka wajabta shi a kan mutanen da ke gabaninku, tsammanin za ku ji tsoron Allah” (183).

Kwanuka kidayayu. To, wanda ya kasance daga gare ku majinyaci ko kuma yana a kan tafiya, sai ya biya adadi daga wasu kwanuka na dabam. Kuma a kan wadanda suke yin sa da wahala akwai fansa, ciyar da matalauci, sai dai wanda ya kara alheri, to shi ne mafi alheri a gare shi. Kuma ku yi Azumi (da wahalar) ne mafi alheri a gare ku, idan kun kasance kuna sani (184).

Shiriya ga mutane da hujjoji bayyanannu daga shiriya da rabewa. To, wanda ya halarta daga gare ku a watan, sai ya azumce shi, kuma wanda ya kasance majinyaci ko kuwa akan tafiya, sai ya biya adadi daga wasu kwanuka na dabam. Allah Yana nufin sauki a gare ku, kuma baya nufin tsanani gare ku, kuma domin ku cika adadin, kuma domin ku girmama Allah a kan Ya shiryar da ku, kuma tsammanin ku, zaku gode (185).

Kuma idan bayiNa suka tambaye ka daga gare ni, to lalle Ni Makusanci ne. Ina karbar kiran mai kira idan ya kira Ni. Saboda haka su nemi karbawaTa, kuma su yi imani da Ni, tsammaninsu, su shiryu (186).

An halatta a gareku a daren Azumi, yin jima’i zuwa ga matanku, su tufa ne a gare ku, kuma ku tufa ne a gare su, Allah Ya sani, lallai ne ku, kun kasance kuna yaudarar kanku. Saboda haka Ya karbi tubarku, kuma Ya yafe muku. To, yanzu ku rungume su, kuma ku nemi abinda Allah Ya rubuta muku. Kuma ku ci kuma ku sha har silili fari ya bayyana a gare ku daga silili baki daga alfijir, sa’an nan kuma ku cika azumi zuwa ga dare. Kuma kada ku rungume su alhali, kuna masu itikafi a cikin masallatai. Wadancan iyakokin Allah ne, don haka kada ku ketare su, kamar haka ne Allah Yake bayyana ayoyinSa ga mutane tsammaninsu, za su yi takawa. (187).

Kada ku ci dukiyoyinku a tsakaninku da karya, kuma ku sadar da ita zuwa ga mahukunta domin ku ci wani yanki daga dukiyoyin mutane da zunubi, alhali kuwa ku, kuna sani. (188) Suratu Bakara.

2. Hikimar wajabta yin azumi

Mu fara da sunan azumi wato “Ramadan”. Ramadan suna ne na watan tara daga watannin Musulunci, shi ne kuma watan da Allah Ya ambace shi karara.

Hikimar da ta sa aka wajabta mana azumi don tsarkake rai ne da kuma sa mata tsoron Allah don ta samu dacewa a gobe Lahira.

3. Ladubba wajibabbu ga mai azumi

1. Wajibi ne ga mai Azumi ya tashi da niyyar cewa azumi ibada ne cikin maganganunsa da aikace-aikacensa.

2. Ya nisanci abubuwan da aka haramta kuma ya tsare ganinsa da jinsa da tafiyarsa daga haramtattun abubuwa. Wadannan wajibi ne ga mai azumi ya kiyaye su idan yana so azuminsa ya karbu a wajen Allah.

4. Abubuwan da ake so ga mai azumi

1. Jinkirta yin sahur.

2. Gaggauta yin buda baki.

3. Yawan karatun Al-Kur’ani mai Girma.

4. Yawaita adu’oi na alheri.

5. Yawaita sadaka.

6. Yawan ambaton Allah da tsarkake Shi da sauran ayyukan alheri.

5. Falalar watan ramadan

1. A cikinsa aka saukar da Al-Kur’ani: Allah Yac e: ‘Watan Ramadan ne aka saukar da Al-Kur’ani a cikinsa.”

2. Ana gafarta zunubi a cikinsa: Annabi tsira da amindn Allah su tabbata a gare shi ya ce: “Wanda ya yi azumin watan Ramadan yana mal imani yana mai neman lada, to an gafarta masa abin da ya gabata na laifufukansa” Imamu Bukhari ne ya ruwaito hadisin.

3. Amsar adu’ar mai Azumi: Annabi (SAW) yace: “Ana karbar addu’ar mutane uku, mai azumi lokacin bude baki, da shugaba mai adalci da wanda aka zalunta”.

4. Daran Lailatul-Kadiri: Allah Ya ce: “Daren Lailatul-kadiri ya fi wata dubu wajen alheri.”

5. Ana daure shaiddanu: Annabi (S.A.W) ya ce “Idan Ramadan ya zo ana daure shaidanu kuma a bude kofofin Aljanna”.

6. Yin Umra a watan Ramadan yana daidai da aikin Hajji.

6. Ma’anar azumi

Abinda ake nufi da azumi “kamewa da barin ci da sha da saduwa da iyali da duk wani abu da zai shiga cikin ciki daga fitowar alfijiri har zuwa faduwar rana. Yin haka daya ne daga cikin rukunan Musulunci guda biyar.

Don haka ne wajibi ne akan Musulmi da Musulma baligai masu hankali kuma da lafiya da za su iya yin Azumi su yi.

Daga CSP Imam Ahmad Adam Kutubi da Muka’ila Usman BT Imam Nigerian Police Force, Zone 7, Police Headkuarter, Abuja

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ramadan watan Ramadan

এছাড়াও পড়ুন:

Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi

Hukumomin a Ƙasar Saudiyya, sun saki wasu ’yan Najeriya uku da aka kama a Jeddah kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi.

Waɗanda aka saki sun haɗa da Hajiya Maryam Hussain Abdullahi, Hajiya Abdullahi Bahijja Aminu, da Malam Abdulhamid Saddieq.

Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu Kano

Sun shafe makonni huɗu a tsare kafin aka tabbatar da cewa ba su da laifi.

A wajen taron manema labarai a Abuja, mai magana da yawun Hukumar Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi (NDLEA), Femi Babafemi, ya ce sakin ya biyo bayan tttaunawa da Shugaban NDLEA, Janar Mohamed Buba Marwa (mai ritaya), tare da Hukumar Hana Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Saudiyya.

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ne, ya bayar da cikakken goyon baya wajen ganin an saki waɗanda aka kama.

Bincike ya gano cewa wasu masu safarar miyagun ƙwayoyi ne a Filin Jirgin Sama na Mallam Aminu Kano, suka ƙwayoyin a jakunkuna waɗanda aka kama.

Mutanen uku da aka kama, sun tashi a jirgin Ethiopian Airlines a ranar 6 ga watan Agusta don yin Umara, amma aka kama su a Saudiyya.

Binciken NDLEA ya kai ga kama wani shugaban masu safarar miyagun ƙwayoyin, mai shekaru 55, Mohammed Ali Abubakar (wanda aka fi sani da Bello Karama).

Hakazalika, hukumar ta kama wasu mutum uku ciki har da ma’aikatan jirgi.

Mutanen da aka kama su ne suka shirya safarar ƙwayoyin a jakunkunan mutane da aka kama a Saudiyya.

NDLEA ta gabatar da shaidun da suka tabbatar da cewa mutanen da aka kama a Saudiyya ba su da laifi.

Sakamakon haka, hukumomin Saudiyya suka sako ɗaya daga cikinsu a ranar 14 ga watan Satumba, sannan suka sako sauran biyun a ranar 15 ga watan Satumba.

Babafemi, ya ce Marwa ya gode wa hukumomin Saudiyya saboda mutunta yarjejeniyar haɗin kai tsakaninsu da Najeriya.

Ya kuma gode wa Shugaba Tinubu da sauran manyan jami’an gwamnati, ciki har da Ministan Shari’a, Ministan Harkokin Ƙasashen Waje, Ministan Sufurin Jiragen Sama, da Mai Bai Wa Shugaba Shawara Kan Harkar Tsaro, saboda gudummuwarsu.

Ya ƙara da cewa wannan lamari ya nuna cewa Najeriya tana tsayawa wajen kare ‘yan ƙasarta a ƙasashen waje kuma ba za ta yadda wani ɗan Najeriya ya sha wahala saboda laifin da bai aikata ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Sabon Tsarin Kula Da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu Da Kananan Yara
  • Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye
  • Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi
  • Iran Ta Bayyana Abubuwan Da Bata Amince Da Su Ba A Jawabin Bayan Taro Na Kungiyar OIC A Birnin Doha
  • Iran da Saudiyya sun bukaci hadin Musulmi game da halin da ake ci a yankin
  • DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin Tinubu
  • NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
  • Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
  • DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu
  • Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta