Leadership News Hausa:
2025-09-18@02:18:14 GMT

Shin Liverpool Za Ta Kai Labari Ba Tare Da Muhammad Salah Ba?

Published: 1st, March 2025 GMT

Shin Liverpool Za Ta Kai Labari Ba Tare Da Muhammad Salah Ba?

Salah ya kasance danwasa na farko a gasar Premier da ya ci ya kuma bayar aka ci a wasanni daban-daban har goma a kaka daya. Sannan shi ne danwasa na farko da ya yi haka a daya daga cikin manyan gasar Turai biyar tun bayan Lionel Messi da ya yi wannan bajinta a kakar 2014-15, inda ya yi wa Barcelona hakan da kwallo 11.

Sai dai babban abin da yake gaban kungiyar kwallon kafa ta Liberpool ko kuma yake ci mata tuwo a kwarya shi ne kasancewar a karshen wannan kakar kwantiragin Muhammad Salah zai kare kuma har kawo yanzu bai sake sabon kwantiragin ba, tunda har yanzu ba su cimma wata yatrjejeniya ba wadda za ta saka ya ci gaba da zama a kungiyar ta Liberpool.

Mai koyuar da ‘yan wasan kungiyar, Arne Slot ya ce kwazon da Mohamed Salah ke yi a wasannin bana, zai kara yin tsada idan Liberpool za ta tsawaita kwantiraginsa kuma dan wasan na tawagar Masar zai cika shekara 33 da haihuwa cikin watan Yuni lokacin da yarjejeniyarsa za ta kare da kungiyar ta Liberpool wadda take buga wasanninta a katafaren filin wasa na Anfield.

To sai dai dan wasan, yana taka rawar gani a kakar nan fiye da bajintar da ya yi a kungiyar a kakar wasa ta 2017 domin shine ya karbi kyautar fitatcen dan wasa a karawar da Liberpool ta doke Manchester City 2-0 ranar Lahadi a Etihad a Premier League kuma hakan ne ya sa Liberpool ta ci gaba da zama ta daya a kan teburin Premier da tazarar maki 11 tsakani da Arsenal ta biyu da tazarar maki 20 tsakani da Manchester City ta hudu.

Muhammad Salah ya ci kwallo 30 a kakar nan 25 daga ciki a Premier League, na farko da yake da hannu a cin kwallo 40 ko fiye da haka a kaka biyu a babbar gasar ta Ingila. Haka kuma shi ne kan gaba mai hannu a cin kwallo 50 a dukkan karawa a bana tsakanin manyan gasar Turai biyar da suka hada da Premier ta Ingila da La liga da Seria A da Lig 1 na faransa da Bundes Liga ta Jamus.

Liberpool tana da wani tsari da take taka tsantsan kan tsawaita yarjejeniya da duk wani dan wasanta da ya kai shekara 30 da haihuwa kuma hakan ne yasa shima dan wasa Birgil Ban Dijk har yanzu kungiyar bata kara masa sabon kwantiragi ba tare da dan wasa Trend Aledandre Arnold dan Ingila, wanda tuni kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid ta shiga tattaunawa da shi domin ya koma kasar Spaniya da buga wasa.

Liberpool, wadda take jan ragamar teburin Premier League ta karbi bakunci kungiyar kwallon kafa ta Newcastle United a ranar Laraba a gasar Premier kuma daga nan za ta je ta buga wasa da kungiyar kwallon kafa ta Paris St Germain wasan zagaye na biyu a gasar cin kofin zakarun turai na Champions League ranar Laraba 5 ga watan Maris.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: kungiyar kwallon kafa ta

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Bayyana Abubuwan Da Bata Amince Da Su Ba A Jawabin Bayan Taro Na Kungiyar OIC A Birnin Doha

Gwamnatin  kasar Iran ta bayyana wasu abubuwan da bata amince da su ba, a jawabin bayan taro na musamman na kungiyar kasashen musulmi ta (OIC) wanda aka gudanar a birnin Doha na kasar Qatar a ranar litinin 15 gawatan Satumba da mukeciki. Sannan ta kara tabbatar da goyon bayanta ga gwagwarmayan da Falasdinawa suke yi da HKI don kwatar kasarsu da ta mamaye.

A cikin wani bayanin da ma’aikatar harokokin wajen kasar Iran ta fitar a yau Laraba, Jumhuriyar Musulunci ta Iran, tana kara jaddada goyon bayanta ga al-ummar Falasdina, kuma tana kara jaddada tir da allawai da kissan kiyashin da HKI take yi a Gaza da kuma sauran yankunan falasdinawa da ta mamaye. Kuma tana godewa mutanen kasar Iran dangane da goyon  bayan da suke bawa Falasdinawa a gwagwarmayansu da HKI.

Dangane da shawarorin da aka gabatar a taron OIC, Iran tana godiya kasashen musulmi da wadanda ba musulmi kan shawarorin da suka gabatar, don warware rikicin Falasdinawa, daga ciki har da “New York Declaration” ta samar da kasashe 2. Da wasu da dama. Amma JMI tana ganin kafa kasashe biyu bazai warware rikicin ba. Tana ganin gudanar da zaben raba gardama, a kasar wanda zai hada da dukkan falasnawa a ko ina suke a ciki da wajen kasar, don zabawa kansu tsari dairin gwamnati da suke su ta demucradiyya. Irab tana ganin samar da kasar Falasdinu a dukkan fadinkasar wacce take da dukkan birnin Qudus a matsayin babban birnin kasar ita ce mafita. Yahudawan da suke son zama su zauna wadanda suke son tafiya su koma kasarsu ta asalali.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label Name* Email* Website Label Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Chadi:  Majalisa ta amince a baiwa shugaban kasa  damar ci gaba da Mulki har karshen rayuwa September 17, 2025 Iran Ta Bukaci Musulmi Su Goyi Bayan Yunkurin Kasa da Ka Na Kauracewa Isra’ila September 17, 2025 Kwamitin bincike na MDD ya zargi Isra’ila da aikata “kisan kare dangi” a Gaza September 17, 2025 Iran da Saudiyya sun bukaci hadin kan Musulmi game da halin da ake a yankin September 17, 2025 Duniya na tir da sabon farmakin Isra’ila kan Gaza September 17, 2025 Akalla Falasdinawa 78 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila a Gaza September 17, 2025 Akalla Falsdinawa 78 Ne Suka Yi Shahada A Yau A Gaza. September 16, 2025 Isra’ila Ta Kai Hari A Tashar Jirgin Ruwan Hudaida Dake Yamen September 16, 2025 Iran Ta Gabatar Da Sabbin Kayayyaki 5 A Wajen Taron kere-kere . September 16, 2025 Iran Ta Bukaci IAEA Tayi Tir Da Harin Da Isra’ila Ta Kai A Tashoshin Nukiyarta. September 16, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka
  • Iran Ta Bayyana Abubuwan Da Bata Amince Da Su Ba A Jawabin Bayan Taro Na Kungiyar OIC A Birnin Doha
  • Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala
  • Tawagar Yan Wasan Damben Gargajiya Ta Iran Ta Zama Zakara A Damben Ta Duniya
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara
  • Fira Ministan Spain: Bai Kamata A Rika Barin “Isr’ila” Tana Shiga Gasar
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi
  • Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff