Leadership News Hausa:
2025-05-25@04:38:56 GMT

Dalilin Dakatar Da Shugaban Ma’aikatan jihar Kano

Published: 28th, February 2025 GMT

Dalilin Dakatar Da Shugaban Ma’aikatan jihar Kano

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya dakatar da Muƙaddashin Shugaban Ma’aikata kuma babban Sakatare na sashin shirye-shirye, Salisu Mustapha, bisa zargin yin kutse a albashin ma’aikatan gwamnati da rashin biyan wasu daga cikinsu.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar daren Alhamis, an bayyana cewa dakatarwar ta fara aiki nan take, tare da umartar Mustapha da ya sauka daga matsayin babban Sakatare don bai wa kwamitin bincike damar gudanar da aikinsa ba tare da katsalandan ba.

Labarin Bukar, Malamin Da Ya Shafe Watanni 20 Ba Tare Da Albashi Ba A Borno Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Zaftare Albashin Ma’aikata

A don ci gaba da gudanar da harkokin ofishin, gwamnan ya nada Malam Umar Muhammad Jalo, Babban Sakatare na bincike, kimantawa da tsare-tsare (REPA), a matsayin sabon muƙaddashin shugaban ma’aikata har sai an kammala bincike.

Wannan matakin na zuwa ne bayan kafa kwamitin mutum bakwai ƙarƙashin Hon. Abdulkadir Abdussalam da ke da wa’adin kwanaki bakwai don gano gaskiyar lamarin.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Kotu Ta Yanke Wa Mutum 5 Hukuncin Ɗaurin Wata 1 Saboda Awakinsu Sun Cinye Bishiyar Gwamnati A Kano

Kotun ta bayyana cewa mutanen sun aikata laifin sakaci da kuma jawo asarar dukiyar jama’a.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Donal Trump Ya Kori Gomomi Daga Cikin Ma’aikata A Majalisar Tsaro Ta Kasar Amurka
  • Dan Asalin Jihar Kano Ya Kafa Tarihin Kirkirar Manhaja Mai Auna Tsayin Bishiya A Faransa
  • ‘Aikin Yan Uba Ne’ — Yahaya Bello Ya Karyata Zargin Sha’awar Takarar Shugaban Kasa A 2027
  • Gwamnan Kano Ya Ceto Dalibai 84 Da Ganduje Yaki Biya Wa Kudin Makaranta A Cyprus
  • NAJERIYA A YAU: Dalilin ’Yan Adawa Na Ƙulla Ƙawance A Ƙarƙashin Inuwar ADC
  • NAJERIYA A YAU: Dalilin ’Yan Adawar Najeriya Na Ƙulla Ƙawance A Ƙarƙashin Inuwar ADC
  • An yi Jana’izar Shugaban Ƙungiyar Masu Shirya Finafinai ta Ƙasa a Zariya
  • Iran Ta Gamsu Da Lokaci Da Wurin Da Za A Gudanar Da Shawarwarinta Da Amurka Zagaye Na Biyar
  • Wani Mutum Ya Harbe Ma’aikatan Ofishin Jakadancin Isra’ila A Birnin Washington Na Amurka
  • Kotu Ta Yanke Wa Mutum 5 Hukuncin Ɗaurin Wata 1 Saboda Awakinsu Sun Cinye Bishiyar Gwamnati A Kano