Gwamnan Kano Ya Bada Umarnin Bincika Zargin Zaftare Albashin Ma’aikatan Gwamnati.
Published: 28th, February 2025 GMT
Gwamna Abba Yusuf na jihar Kano ya yi wani kakkausan gargadi game da rahotannin rashin biyan albashi da rashin biyan ma’aikatan jihar, inda ya bayyana hakan a matsayin tauye hakkin ma’aikata da kuma cin amanar jama’a.
Gwamnan ya bayyana haka ne a lokacin da yake kaddamar da kwamitin bincike mai mutane bakwai, karkashin jagorancin Hon.
Sakataren gwamnatin jiha Alhaji Umar Faruk ya wakilta, ya ce kwamitin ya hada da manyan jami’an gwamnati da masana harkokin kudi da wadanda suka kware a tsarin biyan albashi.
Yace Membobin Kwamitin sune Abdulkadir Abdussalam_ – Shugaban, Kwamishinan Karkara da Ci gaban Al’umma Dr. Bashir Abdu Muzakkari – memba, mai ba da shawara na musamman kan tattalin arzikin dijital, Dr. Aliyu Isa Aliyu – Memba, Darakta-Janar na Ofishin Kididdiga na Jihar Kano.
Dokta Hamisu Sadi Ali, Memba, Babban Darakta Janar na Ofishin Kula da Bashi na Jihar Kano, Hajiya Zainab Abdulkadir – Mamba, Darakta, Cibiyar Kwamfuta ta Jihar Kano, Aliyu Muhammad Sani – Sakatare, Darakta, Bincike da Aiki na Hukumar REPA, Ofishin SSG.
Ummulkulthum Ladan Kailani – zata kasance mataiamakiyar sakataren kwamitin.
Ya ce an baiwa kwamitin kwanaki bakwai don gabatar da cikakken rahoto.
Gwamnan ya kuma tabbatar wa da ma’aikatan gwamnati cewa gwamnatinsa ta himmatu wajen tabbatar da adalci, gaskiya da kuma biyan albashi cikin gaggawa, yana mai gargadin cewa duk wanda aka samu da laifin cin zarafin ma’aikata zai fuskanci mummunan sakamako.
ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Kwamiti
এছাড়াও পড়ুন:
Tsoffin ma’aikatan NECO na neman a biya su bashin haƙƙoƙinsu
Tsoffin ma’aikatan Hukumar Shirya Jarabawar (NECO), da suka yi ritaya na neman a biya su haƙƙoƙinsu da suke bin bashi.
Shugaban ƙungiyar tsofffin ma’aikatan, Dokta Abdullahi Rotimi Williams ne ya bayyana hakan a bikin ƙaddamar da hedikwatar kungiyar a Minna, babban birnin Neja.
Dokta Bashir ya zama shugaban Majalisar Shari’ar Musulunci ta Nijeriya Dokta Bashir ya zama shugaban Majalisar Shari’ar Musulunci ta NijeriyaShugaban ya kuma koka kan yadda gwamnatin Nijeriya ta maida ritaya abin fargaba a wurin ma’aikata saboda tarin ƙalubalen da ke biyo bayan hakan, musamman maƙalewar haƙƙoƙinsu.
“Da yawa tsoron ritaya ake yi yanzu. Don haka wannan ƙungiyar za ta taimaka wajen rage waɗannan matsalolin.
“Babban ƙalubalen da muke fuskanta shi ne na lafiya. Don haka ina roƙon shugaban hukumar da ya tabbatar cewa daga yanzu an kammala shirye-shiryen da suka kamata kafin ma’aikacin NECO ya yi ritaya.”
Ya kuma ce duk da jagororin hukumar na yanzu sun biya wasu daga cikin haƙƙoƙin nasu, ba a kai ga biyan alawus ɗin ƙarin girma ba, da na tafiye-tafiye ba.