Sako daga Alawiyya Jilani Jihar Kano:
Ina gaishe da Mummy da Abba, da kannena Zuhra, Sajida, Alhaji, da dukkanin kawayena na islamiyya dana boko wadanda muka kammala dukka, ina gaida Khadija (Sweet Bala), ina gaishe da Siyama Abdul, ina gaishe da Aunty Hajara da sauran ‘yan’uwa da fatan sakon ya iso gare ku kuma da fatan kun yi juma’a lafiya.
Sako daga Balaraba Ibrahim Jihar Kaduna:
Assalam.. Dan Allah a gaishe mun da Sisi ‘yar fucika uwar tsokana, da Hajiya Hazira, da Aunty Amina mai sakwara, ina gaishe da baby nice, da Binta kwaram da sauran wadanda ban gaisar ba wanda suka sanni.
Sako daga Yusuf Uba Muhammad Jihar Kano:
Haj. Rabi’at dan Allah a mikan sakon gaisuwata zuwa ga Baffa Salisu da abokaina kamar su; Zayyanu, Hassan, Fatuhu, Mansur, Aliyu dan ball, su Idris, Shafi’u dake garin Katsina, Alkhairin Allah ya kai masa, sannan ina gaishe da budurwata Maryam Baby, Allah ya sa ta yi juma’a lafiya.
Sako daga Bilyaminu Ahmad Jihar Kaduna:
Sakona zuwa ga dukkanin al’ummar musulmi ne na fadin duniya, ina gaishe da kowa kuma ina yi mana addu’ar fara azumi lafiya mu gama lafiya dan isar Annabi da alkur’ani.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Kungiyar Abokan Yarjejeniyar M.D.D Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ke Kai Wa Kan Iran
Kungiyar ‘Abokan Yarjejeniyar Majalisar Dinkin Duniya’ ta yi Allah wadai da harin da haramtacciyar kasar Isra’ila ta kai kan Iran
Kasashe mambobin kungiyar aminan yarjejeniyoyin Majalisar Dinkin Duniya sun fitar da wata sanarwa ta musamman inda suka yi kakkausar suka kan wuce gona da irin haramtacciyar kasar Isra’ila ke yi kan Jamhuriyar Musulunci ta Iran.
Sanarwar ta yi la’akari da harin hadin gwiwa ta sama da haramtacciyar kasar Isra’ila ta kaddamar a ranar 13 ga watan Yuni a kan wasu wurare da dama a Iran, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane da jikkata wasu daruruwa da suka hada da mata da kananan yara da masana kimiyya, matakin da ya saba wa Yarjejeniya ta Majalisar Dinkin Duniya da muhimman ka’idojin dokokin kasa da kasa.
‘Yan kungiyar sun kuma yi Allah wadai da harin ganganci kan fararen hula, da wuraren zaman jama’a, da kuma cibiyoyin nukiliyar na zaman lafiya, suna masu gargadin cewa irin wadannan ayyuka na iya haifar da watsuwar kayan aikin kimiyya da zai zama babbar barazana ga rayuwar fararen hula da muhalli.
Kungiyar ta yi kira da a tsaya tsayin daka kan amfani da karfi a kan Iran, tana mai jaddada nauyin da ke wuyan babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya na kiyaye manufofi da ka’idojin Yarjejeniyar Majalisar.
Har ila yau, ta jaddada aikin babban daraktan hukumar ta IAEA na yin Allah wadai da hare-haren da haramtacciyar kasar Isra’ila ke kaiwa kan cibiyoyin nukiliyar Iran.