NAJERIYA A YAU: Yadda Azumi Ke Inganta Lafiyar Jiki
Published: 28th, February 2025 GMT
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Al’ummar Musulmi na yin azumi ne bisa dalilan addini kamar yadda Allah Ya yi umarni don samun lada.
Sai dai daga baya binciken masana kimiyya ya gano cewa bayan lada da ake samu daga yin azumi, akwai wasu alfanu da mai azumi ke samu ga lafiyar jikin shi da suka haɗa da inganta ƙarfi da zurfin tunani zuwa fitar da gurbatattun abubuwa da jiki ba ya bukata.
A taƙaice dai, ba kawai lada mai azumi ke samu ba, har da samun lafiyar jiki da na ƙwaƙwalwarsa.
NAJERIYA A YAU: Halin da jama’a za su shiga idan Kamfanin Kaduna Electric ya ƙi sauraren ma’aikatansa DAGA LARABA: Abin Da Ya Sa Wasu Maza Ba Sa Son HaihuwaShirin Najeriya A Yau na wannan rana zai yi nazari ne kan alaƙar da ke tsakanin yin azumi da kuma lafiyar jikin mutum.
Domin sauke shirin, latsa nan
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: lafiya lafiyar jiki Watan Azumin Ramadan
এছাড়াও পড়ুন:
Shugabannin Hukumomin Watsa Labarai Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya ga Tsohuwar Uwargidan Shugaban Ƙasa Aisha Buhari
Shugabannin Hukumomin Watsa Labarai Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya ga Tsohuwar Uwargidan Shugaban Ƙasa Aisha Buhari
Shugabannin manyan hukumomin watsa labarai na ƙasa Hukumar Rediyon Najeriya (FRCN), Gidan Talabijin na Ƙasa (NTA), da Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) – sun kai ziyarar ta’aziyya ga tsohuwar Uwargidan Shugaban Ƙasa, Hajiya Aisha Buhari, bisa rasuwar mijinta, tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari.
Daraktan Kula da Yankin Arewa maso Yamma na Rediyon Najeriya, Mallam Buhari Auwalu, shi ne ya gabatar da tawagar, inda ya bayyana rasuwar tsohon shugaban ƙasar a matsayin babban rashi ga iyalinsa, Najeriya da ma duniya baki ɗaya.
Yayin ziyarar, Daraktan Sashen Injiniya na Hedikwatar Rediyon Najeriya, Injiniya Sanda Askira, ya roƙi Allah Madaukakin Sarki da ya gafarta wa marigayin kuma ya saka masa da Aljannatul Firdaus.
A madadin dangin marigayin, Dujiman Adamawa, Alhaji Musa Yola, ya nuna godiya ga Daraktocin Janar da sauran tawagar bisa wannan ziyarar ta’aziyya.
Ya ce wannan alamar jajantawa da nuna ƙauna ya zama babban ƙarfafawa ga iyalan marigayin a wannan lokaci na jimami.
Tawagar ta kuma kai ziyarar ta’aziyya ga ɗan uwan tsohon shugaban ƙasa, Alhaji Mamman Daura.
Daraktocin Janar sun bayyana cewa za a ci gaba da tuna tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari bisa gaskiyarsa, ƙaunarsa ga ƙasa da kuma gudunmawarsa wajen cigaban siyasa da tattalin arzikin Najeriya.
Haka kuma, sun yi addu’ar Allah ya baiwa iyalansa haƙuri da ƙarfin zuciya, tare da roƙon ‘yan Najeriya da su ci gaba da rayuwa bisa ƙa’idoji da dabi’un da marigayin ya tsaya kai da fata a kansu.
A nasa bangaren, Alhaji Mamman Daura ya nuna matuƙar godiya bisa ziyarar, yana mai bayyana ta a matsayin abin ƙarfafawa da kuma nuna haɗin kan ƙasa.
Ya gode wa shugabannin hukumomin labarai bisa addu’o’insu da kalamai masu daɗi da goyon baya da suka nuna wa iyalan Buhari a wannan lokaci na juyayi.
Cov/Adamu Yusuf