Kwara ta Raba Littafai Fiye da Dubu 74 Kyauta Ga Dalibai
Published: 28th, February 2025 GMT
Sama da litattafai 73,000 na koyarwa da kayan wasanni, gwamnatin jihar Kwara ta raba wa daliban makarantun firamare da kananan sakandare a fadin jihar.
Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq da yake jawabi a wajen taron raba kayayyakin a Ilorin, ya ce sauran kayayyakin da za a raba sun hada da dakunan karatu na firamare 12,780; guda 100 na kayan ilimi na musamman; 260 na Kula da Yara da sauransu.
Gwamna AbdulRazaq wanda ya samu wakilcin kwamishiniyar ilimi da ci gaban jama’a ta jihar, Hajiya Sa’adatu Modibbo Kawu, ta ce wannan wani shiri ne a cikin jerin shirye-shiryen da gwamnatin ke yi wanda ke nuni da fifikon da take da shi na samar da ilimin boko a jihar.
A cewarsa ra’ayin gwamnati ne cewa zuba jari zai mayar da matsalar yaran da ba su zuwa makaranta ya zama tarihi a jihar.
Gwamna AbdulRazaq ya bayyana cewa rabon litattafan kyauta shine don a rage musu nauyi a kan iyaye saboda tsadar kayan koyarwa a kasuwanni.
Ya ce gwamnatin ta kuma fara daukar malamai aiki akai-akai tare da kara musu girma idan sun cancanta, da kuma inganta abubuwan more rayuwa a makarantu da sauran hanyoyin da za a bi wajen kawo sauyi a fannin.
Gwamnan ya yabawa jami’an hukumar ta UBEC da sauran masu ruwa da tsaki bisa yadda suke ba da goyon baya da jajircewa wajen gudanar da aikin.
A nasa bangaren shugaban kwamitin majalisar dokokin jihar Kwara kan harkokin ilimi, Muhammed Boriya, ya bayyana taron a matsayin wani lokaci mai cike da tarihi na ci gaban ilimi na farko a jihar.
Ya ci gaba da cewa a yanzu jihar ta fice daga munanan abubuwan da suka faru a baya, inda ya ce an cike gibi da dama a bangarori da dama.
A nasa jawabin shugaban hukumar SUBEB ta jihar Kwara, Farfesa Shehu Adaramaja, ya ce raba kayan wasanni za su samar da ingantaccen ilimi da kuma bunkasa ci gaba ga yaran makaranta.
COV/ALI MUHAMMAD RABIU
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Kayan Karatu Kwara
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Sakkwato Ta Sayo Manyan Tan-tan 250 Na Sama Da Naira Biliyan 22
An shawarci gwamnatocin jihohin Sakkwato, Kebbi da Zamfara da su kirkiro hanyoyi na wayar da kan al’umma dangane da shirye-shiryen tallafi da ayyukan ci gaba da gwamnatin tarayya ke aiwatarwa domin bunkasa tattalin arziki da tabbatar da tsaro a yankunansu.
Shugaban sashen kimiyyar zamantakewa na Jami’ar Usmanu Danfodiyo da ke Sakkwato, Farfesa Chika Umar Aliyu, ne ya bayar da wannan shawara yayin gabatar da takarda a wajen taron shekara-shekara na kungiyar Nigerian Institute of Management reshen jihar Sokoto na shekarar 2025, wanda aka hada da gabatar da lambar yabo ga wadanda suka cancanta.
Farfesa Chika ya bayyana cewa, gwamnati tarayya na da shirye-shiryen tallafi da dama da suka hada da na noma, kasuwanci da kuma koyar da sana’o’in hannu domin kara habaka tattalin arzikin ‘yan Najeriya da rage zaman kashe wando, da tayar da hankali musamman matasa a yankin.
Ya jaddada cewa dole ne gwamnatocin jihohi su tallafa wa kokarin gwamnatin tarayya ta hanyar amfani da hukumominsu na jin dadin al’umma domin cimma burin shirye-shiryen.
A jawabinsa wajen taron, kwamishinan noma na jihar Sakkwato, Muhammad Tukur Alkali, ya bayyana cewa gwamnatin jihar ta sayo manyan Tan-tan na noma guda 250 da kayan aikin gona da darajarsu ta kai naira biliyan ashirin da biyu da miliyan dari daya (₦22.1bn), domin tabbatar da wadatar abinci.
A cewar Tukur Alkali, gwamnatin jihar ta hanyar shirye-shiryen inganta rayuwar al’umma, ta samar da sama da ayyukan yi 2,700 a bangaren noma, abin da ke da tasiri mai girma wajen bunkasa noma mai dorewa da ci gaban ababen more rayuwa a karkara.
Daga Nasir Malali