Kwara ta Raba Littafai Fiye da Dubu 74 Kyauta Ga Dalibai
Published: 28th, February 2025 GMT
Sama da litattafai 73,000 na koyarwa da kayan wasanni, gwamnatin jihar Kwara ta raba wa daliban makarantun firamare da kananan sakandare a fadin jihar.
Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq da yake jawabi a wajen taron raba kayayyakin a Ilorin, ya ce sauran kayayyakin da za a raba sun hada da dakunan karatu na firamare 12,780; guda 100 na kayan ilimi na musamman; 260 na Kula da Yara da sauransu.
Gwamna AbdulRazaq wanda ya samu wakilcin kwamishiniyar ilimi da ci gaban jama’a ta jihar, Hajiya Sa’adatu Modibbo Kawu, ta ce wannan wani shiri ne a cikin jerin shirye-shiryen da gwamnatin ke yi wanda ke nuni da fifikon da take da shi na samar da ilimin boko a jihar.
A cewarsa ra’ayin gwamnati ne cewa zuba jari zai mayar da matsalar yaran da ba su zuwa makaranta ya zama tarihi a jihar.
Gwamna AbdulRazaq ya bayyana cewa rabon litattafan kyauta shine don a rage musu nauyi a kan iyaye saboda tsadar kayan koyarwa a kasuwanni.
Ya ce gwamnatin ta kuma fara daukar malamai aiki akai-akai tare da kara musu girma idan sun cancanta, da kuma inganta abubuwan more rayuwa a makarantu da sauran hanyoyin da za a bi wajen kawo sauyi a fannin.
Gwamnan ya yabawa jami’an hukumar ta UBEC da sauran masu ruwa da tsaki bisa yadda suke ba da goyon baya da jajircewa wajen gudanar da aikin.
A nasa bangaren shugaban kwamitin majalisar dokokin jihar Kwara kan harkokin ilimi, Muhammed Boriya, ya bayyana taron a matsayin wani lokaci mai cike da tarihi na ci gaban ilimi na farko a jihar.
Ya ci gaba da cewa a yanzu jihar ta fice daga munanan abubuwan da suka faru a baya, inda ya ce an cike gibi da dama a bangarori da dama.
A nasa jawabin shugaban hukumar SUBEB ta jihar Kwara, Farfesa Shehu Adaramaja, ya ce raba kayan wasanni za su samar da ingantaccen ilimi da kuma bunkasa ci gaba ga yaran makaranta.
COV/ALI MUHAMMAD RABIU
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Kayan Karatu Kwara
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Na Iran Ya Ce: Maganar ‘Yan Sahayoniyya Rudu Ne Maras Amfani
Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci ya bayyana kalaman gwamnatin ‘yan sahayoniyya a matsayin wani rudu da ba shi da amfani da har zai yi tasiri a zaman tattaunawan Iran da Amurka Wanda ba na kai tsaye ba, yana mai cewa duk wani hari ko da karami ne za a kai kan Iran zai zama tamkar tartsatsin wuta da zai iya janyo tashin gobara da zai iya kona yankin gaba daya.
A jawabin da ya gabatar yayin taron kolin majalisar shawarar Musulunci ta Iran a yau Talata, Muhammad Baqir Qalibaf ya bayyana cewa: Firai ministan gwamnatin yahudawan sahayoniyya mai laifi ne mai zubar da jinin fararen hula, saboda neman hana mutuwarsa a fagen siyasa, kuma yanzu yana yin barazana ga al’ummar Iran mai girma. Qalibaf ya yi nuni da cewa, wannan mutum mai rauni yana son canza haryar tafiyarsa a kullum rana saboda tsoron kada a kama shi sakamakon kasancewarsa mai laifi da yafi zama abin ki a tarihin wannan zamani.
Qalibaf ya kara da cewa; Bayan shafe shekaru da dama Netanyahu yana yaudarar kafafen yada labarai, a halin yanzu gwamnatin yahudawan sahayoniyya ta fito fili kuma ta bayyana hakikanin fuskar wannan azzalumi ga duniya, musamman ga matasan Amurka da Turai. Qalibaf ya kara da cewa babu wani abin da wannan gwamnatin ta cimma sai kai hare-haren bama-bamai kan makarantu da asibitoci, kuma ba ta cimma burin da ta ayyana a farkon yakin ba, kuma halin da ake ciki yana da matukar rashin tabbas.