Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-05-01@00:08:16 GMT

Gwamnatin Kwara Ta Kaddamar Da Kwas Ga Dalibai Makarantun 50

Published: 27th, February 2025 GMT

Gwamnatin Kwara Ta Kaddamar Da Kwas Ga Dalibai Makarantun 50

Gwamnatin jihar Kwara ta kaddamar da shirin horas da makarantun firamare da kananan makarantun gwamnati 50 a fadin jihar domin su iya amfani da fasahar ziyyana shafin internet.

 

Da yake gabatar da shirin a madadin Gwamna Abdulrahman AbdulRazaq a Makarantar Sakandare ta Bishop’s Smith Junior Ilorin, babban mai ba gwamna shawara na musamman, Alhaji Sa’adu Salau, ya ce shirin na dijital ya kasance don ƙarfafa fannin ilimi.

 

A cewarsa shirin ya shafi sama da dalibai 150 a kowace makarantu 50 na gwamnati a matakin gwaji.

 

Ya ce idan aka kafa harsashin tsarin zamani, yaran jihar Kwara ba za su koma baya a tsakanin takwarorinsu na duniya ba.”

 

Gwamna AbdulRazaq yace sauran makarantun gwamnati da za su ci gajiyar wannan karimcin a babban birnin kasar sun hada da makarantar Sarauniya Elizabeth, Makarantar Grammar Ilorin, da kuma makarantar firamare ta Sheikh Alimi.

 

A nasa bangaren, mataimaki na musamman ga gwamnan jihar Kwara kan harkokin dijital da kirkire-kirkire, Ishola Kayode, ya ce manufar shirin shi ne tabbatar da cewa daliban makarantun gwamnati ba su koma baya ba a duniyar dijital.

 

Ya ce daliban za su zama masu ilimin zamani, inda ya ce za su iya magance matsalolin da ke addabar al’ummarsu.

 

Ya ce za a fadada shirin bayan tantance bayanan da aka yi.

 

A nata jawabin shugabar makarantar Bishop’s Smith College (Junior Session), Mrs Akanbi Janet Ayoola, ta ce aikin na daya daga cikin mafi kyawun shawarar da gwamnatin jihar ta dauka a zamanin da fasahar sadarwa da fasahar kere-kere suka zama abin bukata na rayuwa.

 

COV/ALI MUHAMMAD RABIU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Kwara

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnan Sokoto Ya Amince Da Sauya Wa Manyan Sakatarori 25 Ma’aikatu A Jihar 

Gwamnatin jihar ta ce, matakin na daya daga cikin kokarin gwamnati mai ci na inganta ayyukanta domin samar da romon dimokuraɗiyya ga al’ummar jihar Sokoto.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati Ta ƙaddamar Da Sabon Shafin Intanet Don Inganta Sayayya A Tsakanin Ma’aikatunta 
  • Gwamnan Sokoto Ya Amince Da Sauya Wa Manyan Sakatarori 25 Ma’aikatu A Jihar 
  • Dokta Bashir ya zama shugaban Majalisar Shari’ar Musulunci ta Nijeriya
  • Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Shirya Fara Tantance ‘Yan Fansho
  • Rashin tsaro: Gwamnan AbdulRahman Ya Gana Da Sarakuna Masu Daraja Ta Daya A Jihar Kwara 
  • Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Binciken Yawaitar Haɗurran Tankokin Man Fetur A Nijeriya 
  • Arsenal Da PSG: Wa Zai Yi Nasara A Gasar Zakarun Turai A Yau?
  • Hajjin 2025: Jihar Kwara Ta Fara Allurar Rigakafi Ga Maniyyata
  • Aikin Hajji: Za A Fara Jigilar Alhazan Jihar Kwara A Ranar 12 Ga Watan Mayu
  • Ma’aikata 240 na karɓar albashi biyu, wasu 217 na amfani da lambar BVN ɗaya a Kano