Ƙungiya ta rage farashin kayan marmari saboda Azumin Ramadan
Published: 26th, February 2025 GMT
Shugaban Kungiyar ’Yan Kasuwa Masu Hada-hadar Kayan Marmari a Jihar Oyo, Walin Ibadan, Alhaji Dauda Shehu ya ce, kungiyar za ta rage farashin kayan marmari domin samun sauƙi ga al’ummar Musulmi a cikin watan Azumin Ramadan.
Ya ce, “kamar yadda muka saba yi a baya a irin wannan lokaci, a bana ma za mu rage farashin kayan marmari kamar dankalin Turawa da karas da kukumba da latas da koren tattasai da ake fataucin su daga wasu jihohin Arewa zuwa Kudancin kasa.
“Za mu yi ragin ne daidai gwargwado daga cikin ribar da muke samu saboda albarkar wannan wata’’, inji shi.
Da yake zagayawa da Aminiya sassa daban-daban na kasuwar kayan marmari ta Benjamin da ke Eleyele a Ibadan babban birnin Jihar Oyo, Alhaji Dauda Shehu ya ce, mun yi wata ganawa ta musamman a tsakaninmu da ’yan kasuwa masu fataucin irin wannan kaya daga jihohin Filato da Kaduna da Kano da Sakkwato.
Ya ce sun amince da yi wa kansu da al’ummar Musulmi adalci wajen sauko da farashin kayan a cikin kwana 30 na watan Azumin Ramadan, domin saukaka wa Musulmi da rage masu radadin tsadar rayuwa a wannan lokaci.
Sai dai ya ce, farashin wadannan kaya za su koma yadda ake sayar da su a baya da zarar watan Azumin ya kare.
Ya ce, “mun yi hakan ne saboda albarkar wannan wata na Ramadan, amma bayan kammala kwana 30 na watan Azumin, ya zama wajibi mu mayar da farashin wannan kaya kamar yadda muke sayarwa a baya domin ci gaba da rage farashin zai iya janyo mana asara.
“Muna daukar matakin rage farashin kayan ne bayan mun rage ribar da ke shiga aljihunmu.
Da yake amsa wata tambaya, Alhaji Dauda Shehu ya ce, “masu sarin irin wannan kaya daga sashen Kudu maso Yamma da suke rububin shigowa cikin wannan kasuwa ta Ibadan a kowane garin Allah Ya waye, mun ba su shawarar daukar matakin rage farashin kayan a garuruwan da suka fito, domin samun sauki ga Musulmi a cikin wannan lokaci.
Ya ce, “tashin farashin irin wannan kaya ba laifin mu ba ne, domin yanayi ne da ya shafi kasa baki daya da ke matukar bukatar ci gaba da addu’o’in rokon Allah samun sauki.”
Alhaji Dauda Shehu ya ce, a yanzu haka ana sauke nau’in irin wannan kaya a cikin manyan motoci uku zuwa biyar a kullum a cikin kasuwar ta Benjamin, inda manya da kananan ’yan kasuwa suke rububin saye domin baje-kolinsu a cikin shagunan cikin gari da masu yawon talla a kan hanyoyin birnin na Ibadan.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Oyo Kayan Marmari Watan Ramadan Alhaji Dauda Shehu ya ce rage farashin kayan irin wannan kaya kayan marmari watan Azumin
এছাড়াও পড়ুন:
Hauhawar farashi ya ragu a watan Agusta — NBS
Hukumar ƙididdigar a Najeriya NBS ta bayyana cewa an samu raguwar hauhawar farashin kaya a watan Agusta idan aka kwatanta da watan Yulin da ya gabace shi.
Cikin sabbin alƙaluman da NBS ta fitar a ranar Litinin sun nuna cewa an samu raguwar kashi 1.76 a watan Agustan saɓanin watan Yulin, wanda ya nuna karo na hudu ke nan a jere hauhawar farashin yana sauka.
NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a Legas Kundin Bajinta na Guinness ya taya Hilda Baci murnaRahoton na hukumar NBS na zuwa ne kwanaki bayan da Shugaba Bola Tinubu ya bayar da umarnin karya farashin kayan abinci ƙasar.
A watanin baya-bayan an riƙa samun raguwar hauhawar farashin kayyaki a ƙasar.
Ko alƙaluman da NBS ta fitar a watan Yuni, ta bayyana cewa hauhawar farashi a Najeriya ya sauka zuwa kashi 22.22 daga 22.97 da aka samu a watan Mayu.
A baya dai dai an yi ta kiraye-kirayen gwamnatin ƙasar ta ɗauki matakan rage hauhawarar farashi domin magance tsadar rayuwa da ake fuskanta a ƙasar.