An Nada Tsoffin Shugabannin Najeriya, Kenya, Da Ethiopia Domin Shiga Tsakani A Rikicin Congo
Published: 26th, February 2025 GMT
A kokarin da ake yin a shawo kan rikicin kasar Jamhuriya imukradiyyar Congo, an nada wasu daga cikin tsoffin shugabannin kasashen Afirka a matsayin masu shiga tsakani domin warware rikicin da yaki ci yaki cinyewa tsakanin ’yan tawayen M23 da gwamnatin Dimokuraɗiyyar Congo.
Hakan kuwa yana zuwa ne bayan da Kungiyoyin raya kasashen gabashi (EAC) da kudancin nahiyar Afirka (SADC) suka yanke shawarar daukar wanan mataki, inda suka nada tsoffin shugabannin Habasha da Kenya da Nijeriya domin sanya idanu a kan batun sulhu a Jamhuriyyar Dimokuradiyyar Congo wanda kullum yake kara ta’azzara, duk kuwa da yarjeniyoyin suhu da dama da aka rattabawa hannu.
Wadannan kungiyoyin EAc da SADC sun nada tsohon shugaban Kenya, Uhuru Kenyatta da tsohon Firai Ministan Habasha, Hailemariam Desalegn da kuma tsohon shugaban Nijeriya Olusegun Obasanjo domin ganin sun taimaka saboda tabbatar da sabuwar yarjejeniyar da kuma yin aiki da ita.
Bangarori na kasa da kasa da suka hada da Majalisar Dinkin Duniya da kuma ita kanta Tarayyar Afirka, sun dauki tsawon shekaru suna fadi tashin ganin sun kawo kan wannan matsala ta Congo, amma lamarin ya ci tura.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
Cikin jadawalin GII na 2025, kasashe masu karanci da matsakaicin kudin shiga 17, sun taka rawar gani fiye da yadda aka yi hasashe, bisa matsayin ci gabansu, yayin da kasashen Afirka dake kudu da hamadar Sahara ke kan gaba, cikin kasashe mafiya samun ci gaban kirkire-kirkire, inda kasashen Afirka ta Kudu, da Senegal da Rwanda ke kan gaba a jerin kasashen shiyyar. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp