A kokarin da ake yin a shawo kan rikicin kasar Jamhuriya imukradiyyar Congo, an nada wasu daga cikin tsoffin shugabannin kasashen Afirka a matsayin masu shiga tsakani domin warware rikicin da yaki ci yaki cinyewa tsakanin ’yan tawayen M23 da gwamnatin Dimokuraɗiyyar Congo.

Hakan kuwa yana zuwa ne bayan da Kungiyoyin raya kasashen gabashi (EAC) da kudancin nahiyar Afirka (SADC) suka yanke shawarar daukar wanan mataki, inda suka nada tsoffin shugabannin Habasha da Kenya da Nijeriya domin sanya idanu a kan batun sulhu a Jamhuriyyar Dimokuradiyyar Congo wanda kullum yake kara ta’azzara, duk kuwa da yarjeniyoyin suhu da dama da aka rattabawa hannu.

Wadannan kungiyoyin EAc da SADC sun nada tsohon shugaban Kenya, Uhuru Kenyatta da tsohon Firai Ministan Habasha, Hailemariam Desalegn da kuma tsohon shugaban Nijeriya Olusegun Obasanjo domin ganin sun taimaka saboda tabbatar da sabuwar yarjejeniyar da kuma yin aiki da ita.

Bangarori na kasa da kasa da suka hada da Majalisar Dinkin Duniya da kuma ita kanta Tarayyar Afirka, sun dauki tsawon shekaru suna fadi tashin ganin sun kawo kan wannan matsala ta Congo, amma lamarin ya ci tura.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Xi Jinping Ya Halarci Kwarya-Kwaryan Taron Shugabannin APEC Na 32 Tare Da Gabatar Da Jawabi

 

Shugaba Xi ya kuma bayyana cewa, cikakken zama na 4 na kwamiti na 20 na JKS ya amince da shirin raya kasa na shekaru biyar-biyar karo na 15. Sin za ta yi amfani da wannan damar don ci gaba da gyare-gyaren tattalin arzikinta, da kuma fadada bude kasuwancinta mai zurfi ga ketare, ta haka za ta ci gaba da ba da sabbin damammaki ga yankin Asiya da Pasifik da sauran kasashen duniya ta hanyar zamanantar da al’ummarta. (Amina Xu)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo October 30, 2025 Daga Birnin Sin Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma  October 30, 2025 Daga Birnin Sin Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC October 30, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka
  • Rikicin PDP: Tsagin Wike ya dakatar da Damagum
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Mayar Da Martani Ga Takwaransa Na Amurka Akan Rikicin Addini
  • Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar
  • Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?
  • Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare
  • Xi Jinping Ya Halarci Kwarya-Kwaryan Taron Shugabannin APEC Na 32 Tare Da Gabatar Da Jawabi
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Daliban Makarantar Kudi Suka Fi Na Gwamnati Kokari
  • Juventus ta ɗauki tsohon kociyan Italiya, Luciano Spalleti
  • Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai