Iyalan Malcolm X sun nemi Trump da ya yi bayani kan makomar batun kisansa
Published: 26th, February 2025 GMT
Iyalan Malcolm X, bakar fata fata kuma daya daga cikin jagororin musulmin Amurka da aka kashe a ranar 21 ga Fabrairun 1965, sun bukaci shugaban Amurka Donald Trump da ya bayyana bayanan da ke da alaka da kashe shi, kamar yadda shafin Arabi 21 ya ruwaito.
Iyalan Malcolm X sun gabatar da bukatar ne a cikin wata sanarwa da Ben Crump, lauya mai kare hakkin bakar fata a Amurka ya bayar, a wani taro da aka gudanar tare da iyalan Malcolm X a birnin New York na kasar Amurka domin cika shekaru 60 da kashe shi.
Crump, ya yi nuni da wani umarni da Trump ya sanya wa hannu a watan Janairu, inda ya bayyana dukkan bayanan da suka shafi kisan gillar John F. Kennedy, da Martin Luther King, Jr., inda ya bukaci Trump da ya bayyana duk wasu bayanai da suka shafi kisan Malcolm X.
Crump ya bayyana fatansa na cewa Trump zai amsa bukatun iyalan Malcolm X. “Muna sa ran Trump zai dauki mataki a ranar 19 ga Mayu, 2025, a bikin cika shekaru 100 da haihuwar Malcolm X,” in ji shi.
A ranar 19 ga Mayu kowace shekara, Amurkawa da yawa suna bikin “Ranar Malcolm X” don girmama shi a matsayin daya daga cikin fitattun masu fafutukar kare hakkin bakar fata a Amurka a cikin shekarun 1960.
Malcolm X ya kasance kwararre wajen Magana da kaifin basira da kuma kwarjini. Amurkawa da dama sun kadu a lokacin da labarin kisansa ya yadu a shekara 1965.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Sarki Sanusi II ya koka kan yawan cin bashin Najeriya
Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II ya koka bisa yawan bashin da Najeriya ke ciyowa da kuma yadda gwamnati ke facaka da kuɗaɗen.
Sarkin wanda tsohon Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN) ne, ya kuma bayyana cewa cire tallafin man fetur da Gwamnatin Tarayya ta yi shi ne mafi alheri, yana mai cewa da Gwamnatin ba ta cire tallafin mai ba, da Najeriya ta daɗe da tsiyacewa.
“Adawata a ɓangaren shan man ne, saboda muna ba da aikin yi ga matatun mai a Turai. Muna ba da aikin ga masu tace ɗanyen man,” in ji Sarki Sanusi.
Da yake jawabi a Taron Adabi na Duniya na Kano (KAPFEST) da aka gudanar a Kano ranar Asabar, masanin tattalin arzikin ya bayyana cewa ɗabi’ar yawan cin bashin Najeriya za ta yi mummunar illa ga tattalin arzikin ƙasar na tsawon lokaci.
Mutuwar majinyata: Asibitin Aminu Kano na roƙon KEDCO ya dawo da wutar lantarki Gidauniyar Misilli ta mayar da yara 150 makaranta a GombeMasanin tattalin arzikin ya bayyana damuwa musamman kan yadda gwamnati ke kashe kuɗaɗen da ta ciyo bashin.
Zuwa ƙarshen watan Maris, yawan bashin da ake bin Najeriya ya haura Naira tiriliyan 150.
A yayin taron wanda cibiyar Poetic Wednesdays Initiative (PWI), ta shirya, Sarki Sanusi II ya ce, ya ce, “Ina muke kai wannan tulin bashin da muke ciyowa a ƙasar nan?
“Zan yi farin cikin ganin an yi amfani da kuɗaɗen a fannin ilmantar da matasanmu, saboda su ne za su biya. Amma bai kamata mu yi ciyo bashi muna lafta wa tattalin arzikin ƙasa ba tare da zuba jari a fannin ilmantar da waɗanda su ne za su biya bashin ba.
“Nan da shekara 20 za mu faɗa a matsala a dalikin cin bashi. Dole a zuba jari a fannin inganta rayuwarsu domin samar da abubuwa.”
Ya bayyana cewa Najeriya ba ta yi sa’ar shugabanni nagari ba a tsawon lokaci, yana mai cewa yawancin shugabannin ƙasar ragwage ne masu yawan kawo uzuri.
Sarki Sanusi II ya bayyana kyakkyawan shugabanci a matsayin muhimmin abin da zai ceto Najeriya daga halin da take ciki, wanda ya kira na rashin sa’a.
Da yake sukar yanayin koma-bayan Najeriya alhali wasu ƙasashe sun yi gaba ta fannin kimiyya da fasaha da ci-gaban zamani, Sarki Sanusi II ya buƙaci matsala da su tashi domin karɓar ragamar shugabancin ƙasar, yana mai jaddada cewa hakan abu mai yiwuwa ne idan matasan suka jajirce.