HausaTv:
2025-07-31@22:25:25 GMT

 HKI: Hamas Ta Sake Gina Kanta A Arewacin Gaza

Published: 25th, February 2025 GMT

Kafafen watsa labarun HKi sun ambato jami’an soja na cewa, mayakan Hamas sun sake gina kansu ta hanyar daukar dubban mayaka, kuma suna nan a arewacin Gaza ba su fita daga ciki ba.

Kafafen  watsa labarun na HKI sun kuma kara da cewa; mayakan da kungiyar take da su a yanzu, sun rubanya mayakanta na baya, kafin barkewar yaki, kuma kungiyar ta koyi darussa daga yaki da sojan kasa na Isra’ila a baya.

Jaridar “Badiot Ahranot” wacce ta dauki labarin ta kuma ce; Har yanzu Hamas ba ta fito da dukkanin mayakanta a filin daga ba, da adadinsu ya kai 30,000, kuma tana ba su albashi ta hanyar kudaden harajin da take karba.

Wani sashen na bayanin kafafen watsa labarun ‘yan sahayoniyar ya kunshi cewa; Hamas ta sake dawo da harkokin tafiyar da sha’anin yankin na Gaza domin sake gina karfinta na soja da tattalin arziki.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Shugabannin Hukumomin Watsa Labarai Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya ga Tsohuwar Uwargidan Shugaban Ƙasa Aisha Buhari

Shugabannin Hukumomin Watsa Labarai Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya ga Tsohuwar Uwargidan Shugaban Ƙasa Aisha Buhari

Shugabannin manyan hukumomin watsa labarai na ƙasa Hukumar Rediyon Najeriya (FRCN), Gidan Talabijin na Ƙasa (NTA), da Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) – sun kai ziyarar ta’aziyya ga tsohuwar Uwargidan Shugaban Ƙasa, Hajiya Aisha Buhari, bisa rasuwar mijinta, tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari.

Daraktan Kula da Yankin Arewa maso Yamma na Rediyon Najeriya, Mallam Buhari Auwalu, shi ne ya gabatar da tawagar, inda ya bayyana rasuwar tsohon shugaban ƙasar a matsayin babban rashi ga iyalinsa, Najeriya da ma duniya baki ɗaya.

Yayin ziyarar, Daraktan Sashen Injiniya na Hedikwatar Rediyon Najeriya, Injiniya Sanda Askira, ya roƙi Allah Madaukakin Sarki da ya gafarta wa marigayin kuma ya saka masa da Aljannatul Firdaus.

A madadin dangin marigayin, Dujiman Adamawa, Alhaji Musa Yola, ya nuna godiya ga Daraktocin Janar da sauran tawagar bisa wannan ziyarar ta’aziyya.

Ya ce wannan alamar jajantawa da nuna ƙauna ya zama babban ƙarfafawa ga iyalan marigayin a wannan lokaci na jimami.

Tawagar ta kuma kai ziyarar ta’aziyya ga ɗan uwan tsohon shugaban ƙasa, Alhaji Mamman Daura.

Daraktocin Janar sun bayyana cewa za a ci gaba da tuna tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari bisa gaskiyarsa, ƙaunarsa ga ƙasa da kuma gudunmawarsa wajen cigaban siyasa da tattalin arzikin Najeriya.

Haka kuma, sun yi addu’ar Allah ya baiwa iyalansa haƙuri da ƙarfin zuciya, tare da roƙon ‘yan Najeriya da su ci gaba da rayuwa bisa ƙa’idoji da dabi’un da marigayin ya tsaya kai da fata a kansu.

A nasa bangaren, Alhaji Mamman Daura ya nuna matuƙar godiya bisa ziyarar, yana mai bayyana ta a matsayin abin ƙarfafawa da kuma nuna haɗin kan ƙasa.

Ya gode wa shugabannin hukumomin labarai bisa addu’o’insu da kalamai masu daɗi da goyon baya da suka nuna wa iyalan Buhari a wannan lokaci na juyayi.

Cov/Adamu Yusuf

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Horas Da Mata 600 Kan Abincin Yara Mai Gina Jiki A Jigawa
  • NNPCL ya sake haƙa sabbin rijiyoyin man fetur 4 a Kolmani
  • Kamfanin NNPCL ya sake haka sabbin rijiyoyin man fetur 4 a Kolmani
  • Tallafin matar Tinubu na N1bn ga ’yan gudun hijirar Binuwai ya bar baya da kura
  • Shugabannin Hukumomin Watsa Labarai Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya ga Tsohuwar Uwargidan Shugaban Ƙasa Aisha Buhari
  • Shugaban Kasar Ivory Coast Ya Bayyana Shirinsa Na Sake Tsayawa Takarar Shugabanci Karo Na Hudu
  • Amincewa Da Kasar Falasɗinu: Birtaniya Ta Gindaya Wa Isra’ila Sharuɗɗa
  • Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa
  • Shugaban Ivory Coast Ouattara zai sake takara wa’adi na huɗu
  • Araqchi: Iran Zata Mayar Da Martanin Da Ba Zai Yiwu A Boye Ba  Kan Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kanta