Ana Zargin Mourinho Da Furta Kalaman Batanci Akan Galatasaray
Published: 25th, February 2025 GMT
Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Galatasaray ta ce za ta fara gudanar da bincike kan kocin Fenerbahce Jose Mourinho bayan da ta zarge shi da furta kalaman wariyar launin fata bayan da ƙungiyoyin suka tashi 0-0 ranar Litinin.
Zuwa yanzu dai ba a bayyana irin kalaman da Galatasaray ke nufin Mourinho da furtawa ba, da yake magana a taron manema labarai bayan kammala wasan derby na Istanbul, Mourinho ya ce kujerar da ya zauna a filin wasan Galatasaray ba ta zama kurum, ta na tsalle kamar biri idan aka zauna kanta, ya kuma sake nanata sukarsa ga alƙalan wasan Turkiyya, yana mai cewa da an tafka babban kuskure idan akayi amfani da wani alkalin wasan ƙasar a wasan.
Ɗan ƙasar Slovenia Slavko Vincic ne ya jagoranci wasan na ranar Litinin bayan ƙungiyoyin biyu sun buƙaci wani jami’in ƙasar waje ya jagoranci wasan, kazalika barazanar ɗaukar matakin shari’a, Galatasaray ta ce za ta gabatar da “ƙorafe-ƙorafe a hukumance” ga hukumomin ƙwallon ƙafan ƙasar Turkiyya.
A cikin wata sanarwa da Galatasaray ta fitar ta ce tun daga lokacin da ya fara gudanar da aikinsa a ƙasar Turkiyya, kocin Fenerbahce Jose Mourinho na ci gaba da furta kalaman batanci ga al’ummar Turkiyya, an nada Mourinho mai shekaru 62 wanda ya lashe gasar zakarun Turai sau biyu a matsayin kocin Fenerbahce a bazarar da ta wuce kuma an dakatar da shi da kuma cin tarar shi a farkon wannan kakar saboda yin Allah wadai da ƙa’idojin alƙalan wasa a Turkiyya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga sun kashe mutum 5 a sabon hari a Alkaleri
Mahara sun kashe akalla mutane biyar a Dajin Madam da ke yankin Karamar Hukumar Alkaleri ta Jihar Bauchi.
Wannan na zuwa ne bayan a makon jiya ’yan bindiga sun kutsa kauyukan da ke kusa da garin Mansur a karamar hukumar, inda suka kashe mutane hudu, suka kwashe kayayyaki a shagunansu.
Daga bisani ’yan sanda sun sun bi su, inda suka fatattake su suka gudu zuwa cikin kungurmin Dajin Madam.
Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Abdulkadir Mohammed ne ya sanar da mutuwar mutanen a yayin taron zaman lafiya da aka gudanar a garin Nahutan Darazo a kokarinsa na sasanta rikicin baya-bayan nan tsakanin manoma da makiyaya da ya yi sanadin jikkatar wassu mutane a Darazo.
Gwamnan ya kuma nuna matuqar damuwarsa kan bisa yadda mafarauta da a baya suke goyon bayan ayyukan tsaro na kare dazuzzukan jihar a yanzu haka suka shiga cikin rikici da manoma.
Wani mutum ya mutu yayin raba faɗar ma’aurata ’Yan sa-kai aƙalla 100 da ’yan sanda 30 sun mutu a bakin aiki a Katsina —GwamnatiGwamna ya ce gwamnatinsa tare da hadin gwiwar hukumomin tsaro da kungiyoyin ’yan banga sun dukufa wajen kwato dabbobin da aka sace da kuma wanzar da zaman lafiya a yankunan karkara.
Ya yaba wa mafarautan yankin bisa ci gaba da goyon bayan da suke bayarwa wajen tabbatar da kare dazuzzukan. “Kun taimaka mana wajen kare dazuzzukanmu a Toro, Ningi, Duguri, Yankari, Kirfi, ba a Darazo kadai ba.
“A ranar Litinin ne ’yan bindiga suka kashe mutane biyar a Dajin Madam, wanda ke kan iyaka da Taraba, Filato, da Bauchi-Alkaleri.
“Me ya sa ba ku taimaka mana a can ba? Muna fuskantar kalubale sosai a dazuzzukanmu. Bauchi tana da dazuzzukan sama da hekta miliyan hudu da tsaunukan da ba kowa zai iya shiga ba, sai ku.”
Gwamna Bala ya alaqanta wannan tashin hankali da kwararowar jama’a daga wasu jihohi zuwa Bauchi, tare da qaruwar yawan jama’a, lamarin da ya qara matsin lamba ga kasa da albarkatun kasa.
Yace Yan bindigan yanzu Suna cikin Jihar Taraba ne,kuma Gwamnan Taraba munyi Magana dashi zamu Yi hadin guiwar Domin a fatattakesu a wurin”
Kan rikicin manoma da makiyaya a Darazo da Sade kuma, gwamna yya kaddamar da wani babban kwamiti da zai binciki rikicin na dajin Aliya, Yautare, da Farin Ruwa na Karamar Hukumar Darazo.
Mataimakin gwamnan jihar, Muhammad Auwal Jatau, wanda kuma shi ne shugaban kwamitin ne ya kaddamar da kwamitin a gidan gwamnati da ke Bauchi, inda ya kuma bukaci ’yan kwamitin da su gudanar da ayyukansu cikin himma, adalci, da rashin son kai.