HausaTv:
2025-06-15@17:34:50 GMT

Birtaniya Da Faransa suna Son  Aikewa Da Sojojin Turai 30,000 Kasar Ukiraniya

Published: 23rd, February 2025 GMT

Jaridar Wall Satreet Journal ta ambaci cewa kasashen Faransa da Birtaniya suna shirya yiyuwar aikewa da sojojin tabbatar da zaman lafiya a cikin kasar Ukiraniya idan an tsagaita wutar yaki.

Jaridar ta Amurka ta kuma kara da cewa; Idan an kai ga cimma tsagaita wutar yaki to da akwai yiyuwar turawan za su aike da sojojin zaman lafiya da za su kai 30,000 daga cikin har da na kasar Switzerland.

Sai dai kuma aiwatar da shirin na turai yana da alaka ne da yadda Donald Trump zai amince da kasarsa ta taka rawa, idan har Rasha ta kai wa turawan hari, ko ta keta yarjejeniyar tsagaita wuta, kamar yadda jaridar ta ambato wani jami’in turai din yana fada.

Jaridar ta kara da cewa turawan ba za su bukaci Amukan ta aike da sojoji tare da su zuwa Ukiraniya din ba, sai dai za su bukaci taimakonta da kayan aikin da ba su da su.

A ranar Alhamis mai zuwa ne ake sa ran cewa Fira ministan Birtaniya Sir Keir Rodney Starmer zai tattauna shirin nasu na turai da shugaban kasar Amurka Donald Trump.

A gefe daya, kwamandan sojojin kasar Switzerland  Laftanar Janar Thomas Sussli ya bayyana cewa, kasarsa za ta iya taimakawa da wani adadi na sojojin zaman lafiya anan gaba,idan har gwamnatin Ukiraniyan ta bukaci hakan.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kakakin Gwamnatin Iran Ta Ce daga Yau Lahadi Wuraren Fakewa A Bude Suke Sa’o’I 24 A Tehran

Kakakin gwamnatin kasar Iran ta bayyana cewa, kasar Iran ta shiga yaki, kuma don haka dole sai an sami sauyi a rayuwar mutane ba. Fatima Muhajirani ta bayyana cewa daga yau ramukan layin dogo a cikin birnin Tehran wuraren mafaka da muyewa ne na mutanen da suke birnin har’ila yau za’a bude masallatai da makarantu don su zama wuraren samun mafaka.

A wani bangare fatimeh Muhajirani ta bayyana cewa an rufe sararin samaniyar kasar Iran, don haka babu jirgi wanda zai tashi a ciki ko wajen kasar har zuwa abinda hali yayi ta kuma kara da cewa a halin yanzu jirgin kasa zai zama hanyarb tafiya mafi sauki a wannan haling a mutane. Tace mahajjan Iran zasu dawo ta hanya daga kasar Iraki bayan sun yada zango a birnin Najaf na kasar Irakin.

Sannan ta bayyana cewa abinci da makamashi da magunguna a asbitoci da dakunan shan magani suna nan isassu a kasar. Amma ta sake nanatawa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Ce Ba’a Rufe Kofar Diblomasiyya Ba, Matukar HKI Ta Dakatar Da Kaiwa Kasar HKI
  • Sojojin Kasar Iran Sun Ce Bazasu Dakatar Da Yaki ba Har Zuwa Samun Nasara A kan HKI
  • Kakakin Gwamnatin Iran Ta Ce daga Yau Lahadi Wuraren Fakewa A Bude Suke Sa’o’I 24 A Tehran
  • ‘Yan Wasa Biyar Da Suka Taka Rawar Gani A Kofin Zakarun Turai
  • Martanin sojojin Iran ga Isra’ila zai zama mafi muni idan aka ci gaba da kai hari (Pezeshkian)
  • Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • Jami’in Hamas Ya Jinjinawa Iran Kan Kakkausan Martanin Da Ta Mayar Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Jagora: Sojojin Iran ba zasu sararawa Isra’ila ba
  • Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai
  • Kamfanonin Waje Sun Ce Dole Ne Su Shiga A Dama Da Su A Cikin Kasuwar Kasar Sin