Gawuna ne ya lashe zaɓen Gwamnan Kano a 2023 — Ata
Published: 23rd, February 2025 GMT
Ƙaramin Ministan Gidaje da Tsara Birane, Yusuf Abdullahi Ata, ya bayyana cewa ɗan takarar Gwamnan Kano na jam’iyyar APC a Zaɓen 2023 Nasiru Yusuf Gawuna ne ya yi nasara.
Sai dai Ministan ya ce ƙaddarar hukunci daga Allah ne ya sanya a yanzu haka ba shi ke riƙe da madafan iko a Jihar Kanon ba.
Jami’ar Sojoji ta BIU ta ƙaddamar da taron magance zamba Za a kafa ƙarin makarantu a Zariya — Abbas TajudeenAta ya faɗi hakan ne yayin da yake barazanar ficewa daga jam’iyyar APC muddin ake sake naɗa Abdullahi Abbas a matsayin shugaban jam’iyyar na Jihar Kano.
Ministan ya ce kalaman da shugaban jam’iyyar ya riƙa furtawa su ne dalilin da Allah Ya ƙwace mulkin jihar daga hannun jam’iyyar duk da cewa ƙarara ita ce ta lashe zaɓen gwamnan jihar a shekarar 2023.
Aminiya ta ruwaito cewa furucin Ministan na zuwa yayin wani taron ƙusoshin jam’iyyar APC na Ƙaramar Hukumar Fagge da aka gudanar a Kano.
A cewarsa, “muna sake jaddada aniyar cewa idan suka dawo mana da shi [Abdullahi Abbas], za mu fice daga jam’iyyar.
“Saboda muddin haka ta kasance babu makawa sai jam’iyyar ta sake shan ƙasa. Ba ma tare da irin waɗannan mutane kuma ko mai za faru ba za mu yi tarayya da waɗannan mutanen ba.”
Ata ya bayyana kalaman da Abdullahi Abbas ya riƙa furtawa a matsayin dalilin da jam’iyyar APC a Kano ta sha ƙasa a Zaɓen 2023 — waɗanda ya bayyana a matsayin lafuza marasa kan gado kuma masu munana ladabi ga Allah.
Ya yi gargaɗin cewa muddin aka sake danƙa wa Abdullahi Abbas ragamar jagorancin jam’iyyar to babu makawa sai ta sake shan ƙasa.
“Mun taso an yi mana kyakkyawar tarbiyya, mun san wane ne Allah. Muna girmama malamai da manya saboda haka ba za mu sauka daga kan wannan tarbiyyar ba.
“Amma idan sun dage cewa lallai sai sun dawo da shi [Abdullahi Abbas], za mu fita mu ƙyale musu jam’iyyar kuma na rantse sai jam’iyyar ta sake faɗuwa.”
Minista Ata ya jaddada buƙatar sauya Abdullahi Abbas da wani jagora mai mutunci da daraja muddin jam’iyyar APC tana da burin samun nasara a Jihar Kano.
Kazalika, ya ce Allah ne Yake bayar da mulki ba tasirin yawan ƙuri’u ko dukiya ba.
“Kuri’u ko kuɗi ba sa bayar da mulki hakazalika mutane ba sa yanke hukunci kan wanda zai jagorance su saboda duk wannan lamari a hannun Allah yake.
“Gawuna ne ya yi nasara amma aka murɗe mana zaɓen. Muka garzaya kotu kuma ta tabbatar da cewa an yi mana maguɗi.
“Amma a ƙarshe wanda yake bayar da mulki ya karɓe daga hannunmu saboda ya nuna mana iyakarmu,” in ji Ata.
Wannan dai shi ne karon farko da Ministan ya fito ƙarara ya soki shugabancin jam’iyyar APC a Kano.
Sai dai ana danganta lamarin da yadda wasu ƙusoshin jam’iyyar ke adawa da naɗinsa a matsayin Minista bayan sauke Abdullahi Tijjani Gwarzo da Shugaba Bola Tinubu ya yi.
Bayanai sun ce gabanin zaɓen 2023 an
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Nasiru Yusuf Gawuna zaɓen 2023 jam iyyar APC
এছাড়াও পড়ুন:
Kotu ta tsige dan majalisar da ya sauya sheka zuwa APC
Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta tsige dan majalisar wakilai, Abubakar Gummi daga kujerarsa saboda sauya sheka daga jam’iyyar PDP zuwa APC.
Gummi yana wakiltar mazabar Gummi/Bukkuyum ta Jihar Zamfara a majalisar wakilai.
An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m An sake kama shi a cikin ’yan fashi kwana 5 da fitowa daga kurkukuMai shari’a Obiora Egwuatu ne, ya yanke hukuncin, inda ya umarci kakakin majalisar wakilai, Tajudeen Abbas, da ya daina amincewa da Gummi a matsayin dan majalisar da ke wakiltar mazabar Gummi/Bukkuyum.
Haka kuma ya umarci hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) da ta shirya sabon zabe cikin kwanaki 30 domin cike gurbin kujerar dan majalisar.
Jam’iyyar PDP tare da shugaban ta na jihar Zamfara, Jamilu Jibomagayaki, ne suka shigar da karar dan majalisar.
Sun ce bai dace Gummi ya ci gaba da zama a kujerar ba bayan barin jam’iyyar da ta tsayar da shi takara.
Gummi, ta bakin lauyansa ya ce ya fice daga PDP ne saboda rikicin cikin gida da jam’iyyar ke fama da shi a matakin kasa da kuma a mazabarsa.
Amma kotu ta yi watsi da wannan hujjar, inda ta bayyana cewa babu takaddama da za ta ba shi damar ya sauya sheka.
A hukuncin da ya yanke, Mai shari’a Egwuatu ya ce ’yan siyasa dole su mutunta zabin jama’ar da suka kada musu kuri’a a karkashin jam’iyyar da ta tsayar da su takara.
Ya ce doka ba ta yadda da dan siyasa ya bar jam’iyyar da ta taimaka masa wajen lashe zabe sannan ya koma wata jam’iyya ba tare da ajiye mukaminsa ba.
Ya kara da cewa kuri’un da aka kada don dan takarar na jam’iyya ne, ba nasa ne na kashin kansa ba.
“Idan mutum yana son sauya sheka, ka da ya dauki amanar jama’ar da ta zabe shi ya tafi da ita,” in ji alkalin.
Kotu ta kuma umarci Gummi da ya daina karbar albashi da wasu hakkoki a matsayin dan majalisa, tare da mayar da duk kudaden da ya karba daga ranar 30 ga watan Oktoba, 2024, zuwa ranar da aka yanke hukuncin.
Haka kuma, ya gabatar da hujjar mayar da kudaden ga kotu cikin kwanaki 30.
Mai shari’a Egwuatu ya kuma ci Gummi tarar Naira N500,000, domin biyan PDP kudaden da ta kashe wajen shigar da kara.