Aminiya:
2025-06-15@14:27:55 GMT

Gawuna ne ya lashe zaɓen Gwamnan Kano a 2023 — Ata

Published: 23rd, February 2025 GMT

Ƙaramin Ministan Gidaje da Tsara Birane, Yusuf Abdullahi Ata, ya bayyana cewa ɗan takarar Gwamnan Kano na jam’iyyar APC a Zaɓen 2023 Nasiru Yusuf Gawuna ne ya yi nasara.

Sai dai Ministan ya ce ƙaddarar hukunci daga Allah ne ya sanya a yanzu haka ba shi ke riƙe da madafan iko a Jihar Kanon ba.

Jami’ar Sojoji ta BIU ta ƙaddamar da taron magance zamba Za a kafa ƙarin makarantu a Zariya — Abbas Tajudeen

Ata ya faɗi hakan ne yayin da yake barazanar ficewa daga jam’iyyar APC muddin ake sake naɗa Abdullahi Abbas a matsayin shugaban jam’iyyar na Jihar Kano.

Ministan ya ce kalaman da shugaban jam’iyyar ya riƙa furtawa su ne dalilin da Allah Ya ƙwace mulkin jihar daga hannun jam’iyyar duk da cewa ƙarara ita ce ta lashe zaɓen gwamnan jihar a shekarar 2023.

Aminiya ta ruwaito cewa furucin Ministan na zuwa yayin wani taron ƙusoshin jam’iyyar APC na Ƙaramar Hukumar Fagge da aka gudanar a Kano.

A cewarsa, “muna sake jaddada aniyar cewa idan suka dawo mana da shi [Abdullahi Abbas], za mu fice daga jam’iyyar.

“Saboda muddin haka ta kasance babu makawa sai jam’iyyar ta sake shan ƙasa. Ba ma tare da irin waɗannan mutane kuma ko mai za faru ba za mu yi tarayya da waɗannan mutanen ba.”

Ata ya bayyana kalaman da Abdullahi Abbas ya riƙa furtawa a matsayin dalilin da jam’iyyar APC a Kano ta sha ƙasa a Zaɓen 2023 — waɗanda ya bayyana a matsayin lafuza marasa kan gado kuma masu munana ladabi ga Allah.

Ya yi gargaɗin cewa muddin aka sake danƙa wa Abdullahi Abbas ragamar jagorancin jam’iyyar to babu makawa sai ta sake shan ƙasa.

“Mun taso an yi mana kyakkyawar tarbiyya, mun san wane ne Allah. Muna girmama malamai da manya saboda haka ba za mu sauka daga kan wannan tarbiyyar ba.

“Amma idan sun dage cewa lallai sai sun dawo da shi [Abdullahi Abbas], za mu fita mu ƙyale musu jam’iyyar kuma na rantse sai jam’iyyar ta sake faɗuwa.”

Minista Ata ya jaddada buƙatar sauya Abdullahi Abbas da wani jagora mai mutunci da daraja muddin jam’iyyar APC tana da burin samun nasara a Jihar Kano.

Kazalika, ya ce Allah ne Yake bayar da mulki ba tasirin yawan ƙuri’u ko dukiya ba.

“Kuri’u ko kuɗi ba sa bayar da mulki hakazalika mutane ba sa yanke hukunci kan wanda zai jagorance su saboda duk wannan lamari a hannun Allah yake.

“Gawuna ne ya yi nasara amma aka murɗe mana zaɓen. Muka garzaya kotu kuma ta tabbatar da cewa an yi mana maguɗi.

“Amma a ƙarshe wanda yake bayar da mulki ya karɓe daga hannunmu saboda ya nuna mana iyakarmu,” in ji Ata.

Wannan dai shi ne karon farko da Ministan ya fito ƙarara ya soki shugabancin jam’iyyar APC a Kano.

Sai dai ana danganta lamarin da yadda wasu ƙusoshin jam’iyyar ke adawa da naɗinsa a matsayin Minista bayan sauke Abdullahi Tijjani Gwarzo da Shugaba Bola Tinubu ya yi.

Bayanai sun ce gabanin zaɓen 2023 an

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Nasiru Yusuf Gawuna zaɓen 2023 jam iyyar APC

এছাড়াও পড়ুন:

Ƙwazo da juriya suka sa na zura ƙwallaye 10 a wasanni 10 – Mane

Sadeeƙ Umar da ake yi wa laƙabi da Mane, matashin ɗan wasan ƙwallon ƙafa ne da yake tashen taka leda a rukunin ’yan dagaji a Jihar Kano.

Matashin, wanda tauraronsa ke haskawa a fagen tamola ya yi fice ne bayan da ya kafa wani sabon tarihi na zura ƙwallaye 10 a raga a wasanni 10 da ya buga tare da ba da taimako sau 6 wajen wasu ƙwallayen a rukuni gasar wasannin ’yan dagaji aji 1 da aka fi sani da Amateur 1 a Jihar Kano.

An ciro gawarwaki sama da 200 daga jirgin Indiya da ya yi hatsari Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Zulum ya yi wa fursunoni 66 afuwa

A cikin tattaunawarsa da Aminiya, Sadeeƙ Mane ya bayyana cewa, ƙwazo da sadaukar da kai ne suka taimaka masa wajen kafa wanna tarihi.

Sadeeƙ, wanda kamar sauran ‘yan wasa ya fara buga ƙwallon ne a cikin unguwa kafin daga bisani ya fara buga wa ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Togo da ke Unguwar Birget, Ƙaramar Hukumar Nasarawa a Jihar Kano.

Daga ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Togo, Sadeeƙ ya koma taka leda a ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Legend FC, inda a can ne bayan ya nuna bajinta a Gasar Cin Kofin Shugaban Ƙaramar Hukumar Nasarawa, Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa ta SBS Waliyya da ke buga wasa a matakin Amauteur 1 ta ɗauke shi.

A kakar bana Saƙeeƙ ya kafa tarihi, inda ya buga wasanni goma kuma ya zura ƙwallaye goma a raga.

Wannan nasara da ya samu ta sa ya lashe kyautar ɗan wasan da ya fi kowanne ɗan wasa zura ƙallaye a raga a wannan shekara.

Haka kuma an zaɓi Saƙeed a matsayin ɗan wasan da ya fi kowanne ɗan wasa ƙwarewa a wannan matakin.

Da yake ƙarin bayani kan yadda ya samu nasarar zura ƙwallaye 10 a cikin wasanni 10, Sadeeƙ ya ce, “na buga wasanni 10 kuma na zura ƙwallaye 10 a ragar abokan karawa.

A cikin wasanni 10 ɗin na zura ƙwallayen ne a wasanni 8, wato wasa 2 kacal ne ban ci ƙwallo ba. Wannan ne ya sa na zama ɗan wasan da ya fi zura ƙwallo a gasar.”

Da yake amsa tambayar ko me ne sirrin wannan nasarori haka?

Sadeeƙ Umar sai ya ce: “Ka san an ce in ka ji wane ba banza ba, wato in ba a sha gumi ba a sha rana. Don haka na jajirce ne da ba wa kaina horo da kuma sanya juriya a zuciyata. Wato ina nufin bayan horon da ake yi mana a filin wasa, ni a karan kaina ina fita, in yi gudu da dadare da sauran wasanni na motsa jiki masu wahala don in saba wa kaina,” in ji Mane.

Ya ƙara da cewa, “wannan shi ya sa za ka ga in na shiga fili bana gajiya har a tashi. Haka kuma, wannan shi ne dalilin da ya sa ake yi min laƙabi da shahararren ɗan wasan ƙasar Senegal ɗin nan mai suna Sadio Mane, wato ganin irin salon wasanmu ɗaya ne, kai har ma wasu na cewa, wai mun yi kama ko a fuska.”

Sadeeƙ Mane ya bayyana wa Aminya cewa, burinsa shi ne wata rana ya zama kamar Sadio Mane wato ya fita ƙasashe Turai, ya buga wa manyan ƙungiyoyin ƙwallo ƙafa na duniya wasa.

“Kamar kowane matashin ɗan ƙwallo, ni ma babban burina shi ne in buga ƙwallo a ƙasashen Turai, in shahara kamar Sadio Mane. Ina ji a raina wata rana zan buga wa manyan ƙungiyoyi kamar Chealsea da Liɓerpool da Barcelona,” in ji matashi ɗan wasan.

Sai dai Sadeeƙ ya bayyana cewa, ba kamar sauran matasan ’yan ƙwallo ba da suke son shiga Turai gaba-gaɗi, shi yana da burin ya buga wa ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars kafin ya tafi ƙasashen Turai da ƙwallo.

“A gaskiya ni in so samu ne, na fi son in fara buga wa Kano Pillars wasa kafin in je Turai. Saboda tunda na taso, ina son Pillars sosai. Haka kuma ina ga a matsayina na ɗan Kano zai zamo abin alfahari a gare ni a ce wata rana na sanya wa ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillar riga, na ba da tawa gudunmawar,” in ji Mane.

Mane ya bayyana rashin samun haɗuwa da manajan masu ɗaukar matasan ‘yan wasa zuwa ƙasashen Turai, musamman a jihohin Arewa a matsayin wani babban ƙalubale da matasan ‘yan wasa masu hazaƙa ke gamuwa da shi a wannan yanki.

“Babban ƙalubalenmu a nan Kano da sauran jihohin Arewa shi ne wa zai taimake ka, ya haɗa kai da manajan da suke ɗaukar matasan ‘yan wasa zuwa Turai. Ka ga muna da matasa masu ƙwazo da basira sosai, sai dai ba ma samun wannan gatan. Ban san dalilin da ya sa manajojin ɗin ba sa son zuwa nan ba,” In ji Sadeeƙ Mane.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Masu ƙwacen waya sun kashe ma’aikacin Jami’ar Northwest a Kano
  • Iran ta sake kai hare-haren martani kan Isra’ila
  • Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya
  • Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawar mutum bayan kwanaki 8
  • Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawa guda bayan kwanaki 8
  • Ambaliya: Gwamnatin Kano ta fara tsaftace magudanan ruwa
  • Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6
  • Gwamnan Gombe Ya Yi Allah Wadai Da Kisan Da ‘Yan Daba Suka Yi Wa Amadi Kasiran
  • Leroy Sane ya koma Galatasaray
  • Ƙwazo da juriya suka sa na zura ƙwallaye 10 a wasanni 10 – Mane