Aminiya:
2025-05-01@00:27:16 GMT

Gobara ta ƙone gidaje, amfanin gona da dabbobi a Borno 

Published: 23rd, February 2025 GMT

Wata gobara ta tashi a ƙauyen Bukar da ke Ƙaramar Hukumar Konduga a Jihar Borno, ta yi ɓarna mai tarin yawa.

Gobarar ta lalata gidaje, amfanin gona, da dabbobi na miliyoyin Naira, amma babu wanda ya rasa ransa.

’Yan bindiga sun harbe fasto, sun sace wasu a coci Gawuna ne ya lashe zaɓen Gwamnan Kano a 2023 — Ata

Wani mazaunin ƙauyen ya ce gobarar ta fara ne daga wutar girki a wani gida, sai iska mai ƙarfi ta bazata zuwa wasu gidaje, lamarin da ya sa mutane suka kasa shawo kanta.

Bayan kamawar wutar, sojojin Najeriya da ke yankin sun garzaya domin kai ɗauki.

Sun taimaka wajen kashe wutar tare da ceton tsofaffi da yara.

Kazalika, gobarar ta cinye wani ɓangare na kasuwar ƙauyen, inda ta ƙone shaguna da rumfunan abinci.

Mazauna ƙauyen sun ce yanayin iskar da ake yi a lokacin ya ƙara ta’azzara gobarar, hakan ya sa aka wahala wajen kashe ta.

Duk da hatsarin da ke tattare da wutar, sojoji sun taimaka wajen daƙile gobarar, wanda ya hana ta bazuwa zuwa wasu wurare, ciki har da makarantar ƙauyen.

Shugabannin yankin sun nuna godiyarsu ga sojojin da suka kawo musu ɗauki cikin gaggawa.

“Ba don taimakon Allah da na sojoji ba, gobarar na iya haddasa asarar rayuka,” in ji wani mazaunin ƙauyen, Bukar Usman.

A halin yanzu, Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Borno (SEMA), ta tura tawaga domin tantance asaea tare da raba kayan agaji ga waɗanda gobarar ta shafa.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Sabbin Bayanai Kan Fashe-Fashe Wasu Abubuwa A Tashar Jiragen Ruwan Kasar Iran

Gwamnan lardin Hormozgan (mai hedikwata a Bandar Abbas), Mohammad Ashouri, ya ce wani bangare na lamarin tashar jiragen ruwa na Shahid Raja’i ya faru ne sakamakon keta sanarwar adana kayayyaki ne, wani bangaren kuma na da alaka da sakaci da rashin kulawa (a wajen ajiya).

AShouri, wanda ya bayyana ta hanyar faifan bidiyo a wata hira da aka watsa ta talabijin a yammacin jiya Litinin, ya bayyana sabbin alkaluman wadanda suka bata: Akwai mutanekusan 22 da suka bace, kamar yadda wasu gawarwakin mutane 22 ba a iya tantace su ba ko su waye ba.

Ya ce: “Wasu daga cikin wadanda suka jikkata an hanzarta jigilar su ta jirgin saman soja zuwa asibitin birnin Shiraz.”

Gwamnan lardin Hormozgan na Iran ya ce: An cimma wasu bincike na farko dangane da yiyuwar yin sakaci a wannan fanni, kuma ana gudanar da bincike sosai kan dukkan al’amuran da suka faru. Kuma babu wata daga kafa da za a yi ga duk wanda aka samu da yin sakaci a kan haka za a tuhume shi kamar yadda shari’a ta tanada.

 Ya ci gaba da cewa, “Ta hanyar nazarin faifan bidiyo daban-daban na aukuwar lamarin tashar jirgin ruwa ta Shahid Raja’i, an lura da cewa, an yi jigilar kaya a lokacin da lamarin ya faru, inda hayaki ke tashi, sai kuma fashewar wani abu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Najeriya Wajen Yin Watsi Da Kariyar Cinikayya Da Yin Adawa Da Danniya Da Cin Zarafi
  • Amurka ta sake laftawa wasu kamfaninin mai na Iran takunkumi
  • Za A Yi Allurar Rigakafi Ga Dabbobi Sama Da Miliyan Daya A Babura
  • ISWAP ta ɗauki alhakin kashe mutum 26 a Borno
  • Sabbin Bayanai Kan Fashe-Fashe Wasu Abubuwa A Tashar Jiragen Ruwan Kasar Iran
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kutsa Cikin Quneitra Na Kasar Siriya Tare Da Kafa Shingen Bincike
  • Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno
  • Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok
  • Boko Haram Sun Hallaka ‘Yan Zaman Makoki 7, Sun Jikkata Wasu A Borno
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jadadda Cewa: Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kan Iran Zai Fuskanci Mayar Da Martani