Aminiya:
2025-07-31@14:03:50 GMT

Gobara ta ƙone gidaje, amfanin gona da dabbobi a Borno 

Published: 23rd, February 2025 GMT

Wata gobara ta tashi a ƙauyen Bukar da ke Ƙaramar Hukumar Konduga a Jihar Borno, ta yi ɓarna mai tarin yawa.

Gobarar ta lalata gidaje, amfanin gona, da dabbobi na miliyoyin Naira, amma babu wanda ya rasa ransa.

’Yan bindiga sun harbe fasto, sun sace wasu a coci Gawuna ne ya lashe zaɓen Gwamnan Kano a 2023 — Ata

Wani mazaunin ƙauyen ya ce gobarar ta fara ne daga wutar girki a wani gida, sai iska mai ƙarfi ta bazata zuwa wasu gidaje, lamarin da ya sa mutane suka kasa shawo kanta.

Bayan kamawar wutar, sojojin Najeriya da ke yankin sun garzaya domin kai ɗauki.

Sun taimaka wajen kashe wutar tare da ceton tsofaffi da yara.

Kazalika, gobarar ta cinye wani ɓangare na kasuwar ƙauyen, inda ta ƙone shaguna da rumfunan abinci.

Mazauna ƙauyen sun ce yanayin iskar da ake yi a lokacin ya ƙara ta’azzara gobarar, hakan ya sa aka wahala wajen kashe ta.

Duk da hatsarin da ke tattare da wutar, sojoji sun taimaka wajen daƙile gobarar, wanda ya hana ta bazuwa zuwa wasu wurare, ciki har da makarantar ƙauyen.

Shugabannin yankin sun nuna godiyarsu ga sojojin da suka kawo musu ɗauki cikin gaggawa.

“Ba don taimakon Allah da na sojoji ba, gobarar na iya haddasa asarar rayuka,” in ji wani mazaunin ƙauyen, Bukar Usman.

A halin yanzu, Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Borno (SEMA), ta tura tawaga domin tantance asaea tare da raba kayan agaji ga waɗanda gobarar ta shafa.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Sojojin HKI Sun Ci Gaba Da Kashe Kawunansu

A cikin kwanakin bayan nan ana samun karuwar sojojin HKI da suke kashe kawunansu saboda tabuwar kwakwalensu sanadiyyar yakin Gaza.

Kafafen watsa labarun HKI sun kunshi rahotanni da suke bayani akan yadda sojojin mamayar da su ka yi yaki a Gaza, suke samun tabuwar hankali, da hakan yake sa su kashe kawukansu bayan sun baro Gaza.

Wasu rahotannin sun ambaci cewa, sojojin na HKI suna rayuwa ne a cikin tsaro da ranaza saboda munanan ayyukan da su ka aikata marasa kyau.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojan Amurka Ya Bada Ruwayar Yadda Sojojin Sahayoniyya Suka Kashe Wani Yaro Balasdine
  • Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega
  • Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 
  • Tinubu ya naɗa sabon shugaban hukumar kashe gobara ta ƙasa
  • ’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina
  • An shawarci Manoman Kwara Da Su Yi Taka-Tsan-Tsan Saboda Hasashen Ruwa Da Tsawa A Jihar
  • Sojojin HKI Sun Ci Gaba Da Kashe Kawunansu
  • ‘Yan Sanda A Kano Sun Kama Kasurgumin Dan Fashin Nan Barga Da Wasu Mutum 14
  • Araqchi: Iran Zata Mayar Da Martanin Da Ba Zai Yiwu A Boye Ba  Kan Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kanta
  • Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje