Aminiya:
2025-08-02@05:11:25 GMT

Fasinjoji 4 sun rasu yayin da bas ta kama da wuta a Jigawa

Published: 23rd, February 2025 GMT

Mutane huɗu sun rasa rayukansu, wasu 10 kuma sun samu raunuka bayan wata motar bas ƙirar Hummer ta kama da wuta a garin Gwaram da ke Jihar Jigawa.

Lamarin ya faru da misalin ƙarfe 4 na yammacin ranar Asabar, a kusa da makarantar sakandaren gwamnati ta Government Girls Unity Secondary School da ke Gwaram.

Gobara ta ƙone gidaje, amfanin gona da dabbobi a Borno  Za a kafa ƙarin makarantu a Zariya — Abbas Tajudeen

Kakakin ’yan sandan Jihar Jigawa, SP Lawan Adam, ya tabbatar da faruwar hatsarin cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi.

Ya ce motar ta taso daga Ƙaramar Hukumar Zaki daga Jihar Bauchi zuwa ƙauyen Ribadi da ke Ƙaramar Hukumar Gwaram.

Sanarwar ta bayyana cewa motar na ɗauke da fasinjoji 44, wanda suka haɗa da manya 25 da yara 19.

Kakakin, ya ce wutar ta samo asali ne daga katifa da aka ɗaure a bayan motar, kusa da bututun fetur.

Mutum 10 da suka samu raunuka an garzaya da su asibitin Gwaram, yayin da aka ceto sauran fasinjojin ba tare da sun ji ciwo ba.

Waɗanda suka rasu sun haɗa da Zuwairah Hassan mai shekaru 40, Fatima Hassan mai shekaru biyar.

Sauran sun haɗa da Iyatale Hassan mai shekaru uku da Halima Muhammad mai shekaru 10, dukkaninsu ‘yan ƙauyen Saldiga da ke Ƙaramar Hukumar Zaki, a Jihar Bauchi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Hatsari Jigawa rasuwa mai shekaru

এছাড়াও পড়ুন:

Amincewa Da Kasar Falasɗinu: Birtaniya Ta Gindaya Wa Isra’ila Sharuɗɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer ya shimfiɗa wa Isra’ila wasu jerin sharuɗan da ya ce idan ba ta cika ba, Birtaniya za ta amince da ƙasar Falasdinu.

A ranar Talata ne Mista Starmer ya ce idan har Isra’ila ba ta cika waɗannan sharuɗa ba zuwa watan Satumba Birtaniya za ta amince da ƙasar Falasɗinu.

Sharuɗɗan da firaministan ya gindaya sun haɗa da:

Amincewa da yarjejeniyar tsagaita wuta Bai wa Majalisar Dinkin Duniya damar sake shigar da agaji Gaza Amincewa da yuarjejeniyar zaman lafiya na dogon lokaci wanda zai ”samar da ƙasashe biyu” Tabbatar da cewa ba za a ci gaba da ƙwace Gaɓar Yamma da Kogin Jordan da aka mamaye ba

Haka kuma Keir Starmer ya kuma sake jaddada buƙatun da Birtaniya ke da su kan Hamas da suka haɗa da:

Amincewa da yarjejeniyar tsagaita wuta Sakin duka sauran Isra’ilawan da take riƙe da su Amincewa ba za ta saka hannu a tafiyar da gwamnatin Gaza ba Miƙa duka makamanta

BBC/Hausa

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Haɗarin tirela ya yi sanadin asarar awaki sama da 100 a Zariya
  • An ceto mutum uku da aka yi garkuwa da su a Kebbi
  • Ɗaliban da aka sace a Binuwai sun kuɓuta 
  • Tinubu Ya Cika Alƙawurran Da Ya Ɗauka – Ƙungiyar Gwamnonin Arewa
  • Osimhen Ya Kammala Komawa Galatasaray
  • Sarkin Gudi na Jihar Yobe, Isa Bunuwo Ibn Khaji ya rasu
  • Mutum 9 sun rasu a hatsarin kwale-kwale a Jigawa
  • Kwara Ta Kwashe Mabarata Daga Titunan Jihar Su 94
  • Shugaban hukumar zabe ta jihar Bauchi ya rasu
  • Amincewa Da Kasar Falasɗinu: Birtaniya Ta Gindaya Wa Isra’ila Sharuɗɗa