Leadership News Hausa:
2025-06-15@07:49:57 GMT

Ministan Yaɗa Labarai Ya Taya Gwamna Bago Murnar Cika Shekara 51

Published: 23rd, February 2025 GMT

Ministan Yaɗa Labarai Ya Taya Gwamna Bago Murnar Cika Shekara 51

“Jajircewar sa ga haɓaka ababen more rayuwa, noma da ƙarfafa matasa yana ci gaba da mayar da Jihar Neja abin koyi wajen cigaba da wadata.”

 

Ministan ya ce yana taya gwamnan na jihar su murna, yana mai bayyana shi a matsayin jagora mai kishin hidimta wa al’umma da cigaban ƙasa.

 

Idris ya ƙara da cewa, “Yayin da yake bikin wannan rana ta musamman, ina taya shi murna a matsayin jagora wanda jajircewar sa ga hidima da shugabanci ke nuna ainihin cigaba.

 

“Ina roƙon Allah ya ci gaba da ba shi lafiya, hikima da ƙarfi don ya ci gaba da tafiyar da Jihar Neja zuwa matakai mafi girma.”

 

Ya kammala da taya Gwamna Bago murna, inda ya ce, “A karo na biyu, muna taya ka murna da fatan alheri a wannan rana mai albarka, Mai Girma Gwamna!”

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Iran ta caccaki kudurin IAEA wanda ta ce yana cike da siyasa

Iran ta yi Allah-wadai da wani kuduri da ta danganta da na siyasa da hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA ta dauka, tana mai cewa ba shi da tushe na fasaha ko doka.

Hukumar kula da makamashin nukiliya ta Iran (AEOI) da ma’aikatar harkokin wajen kasar sun fitar da sanarwar hadin gwiwa yau Alhamis bayan da majalisar gwamnonin hukumar ta IAEA suka amince da wani kuduri da ke zargin Iran da rashin cika alkawuran da ta dauka na nukiliya.

Kuri’u 19 ne suka amince da kudurin wanda Amurka da Birtaniya da Faransa da Jamus suka tsara.

Kasashen Rasha, China da Burkina Faso sun kada kuri’ar kin amincewa da shi, Yayin da kasashen Afirka ta Kudu, Indiya, Pakistan, Masar, Indonesia da Brazil suka ce su kam ba ruwan su.

Sanarwar da Iran ta fitar dangane da wannan kudiri ta ce, Jamhuriyar Musulunci ba ta da wani zabi face mayar da martani ga wannan kudiri na siyasa.”

Sanarwar ta ce, Shugaban Hukumar Makamashin Nukiliya ta Iran (AEOI), Mohammad Eslami, ya ba da umarnin gina sabuwar cibiyar tace uranium a wani wuri mai aminci.

Sabuwar cibiyar za ta kunshi sabbin na’urorin tace uranium na zamani inji sanarwar.

A cikin sanarwar, Tehran ta yi tir da kudirin na “siyasa da son zuciya” na IAEA  Wanda Amurka da manyan kasashen Turai uku – Faransa, Jamus da Birtaniya suka tsara.

Iran ta kuma yi tir da shirun da Amurka da kawayenta na Turai suka yi wajen tinkarar yadda gwamnatin Isra’ila ke ci gaba da kin mutunta yarjejeniyar hana yaduwar makaman kare dangi.

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da Iran da Amurka suka tabbatar da sake ganawa a karo na shida a ranar Lahadi mai zuwa game da shirin nukiliyar Iran wanda a’a gudanar a birnin Muscat a shiga stakanin kasar Oman.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • Wutar Lantarki Mai Ƙarfi Ta Yi Ajalin Mutum Biyar A Gombe
  • Iran : Halin da ake ciki ba zai iya bada damar tattaunawa da Amurka ba
  • Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai
  • Xi Ya Yi Kira Da A Kara Azamar Gina Kasa A Gabar Da Ake Bikin Cika Shekaru 120 Da Haihuwar Dan Mazan Jiya Chen Yun
  • Iran ta caccaki kudurin IAEA wanda ta ce yana cike da siyasa
  • Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Zulum ya yi wa fursunoni 66 afuwa
  • Ba Zan Bar Nijeriya Ta Zama Kasa Mai Jam’iyya Daya Ba – Tinubu
  • Ranar Dimokuraɗiyya: Gwaman Zulum ya yi wa fursunoni 66 afuwa
  • Sojoji Sun Kashe Auta, Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda Da Wasu 13 a Jihar Zamfara