Gwamnatin Filato ta dakatar da haƙar ma’adinai saboda matsalar tsaro
Published: 21st, February 2025 GMT
Gwamnan Jihar Filato, Caleb Mutfwang, ya bayar da umarnin dakatar haƙar ma’adanai a faɗin jihar daga ranar 21 ga watan Fabrairu, 2025.
Ya yanke wannan shawara ne saboda ayyukan haƙar ma’adanai ba bisa ƙa’ida wanda ke da alaƙa da laifuka da suka shafi ta’addanci, satar mutane, da fataucin miyagun ƙwayoyi.
Haka kuma, ya ce yawan baƙi da ke shiga yankunan da ake haƙar ma’adanai na ƙara haddasa matsalar tsaro.
“Akwai ƙaruwar ayyukan haƙar ma’adanai ba bisa ƙa’ida ba, wanda ke haifar da matsalolin tsaro a sassa daban-daban na jihar.
“Haka kuma, yawan baƙin da ke shiga yankunan haƙar ma’adanai na ƙara yawan laifuka kamar ta’addanci, garkuwa da mutane, da fataucin miyagun ƙwayoyi,” in ji Gwamna Mutfwang.
Domin shawo kan wannan matsala, gwamnatin ta kafa kwamitin da zai binciki waɗanda ke da izinin haƙar ma’adanai da kuma ƙirƙirar tsarin kula da ayyukan haƙar.
Gwamnan ya ƙara da cewa za su yi aiki tare da Gwamnatin Tarayya domin tabbatar da tsare-tsaren doka da kuma inganta matakan tsaro.
“Za mu haɗa kai da Gwamnatin Tarayya domin bitar yadda ake sanya ido kan ayyukan haƙar ma’adanai.
“Haka kuma, za mu tabbatar da cewa kamfanonin haƙar suna bai wa al’umma gudunmawa,” in ji shi.
Gwamnan ya yi alƙawarin duba matsalar tsaro a yankunan da ake haƙar ma’adanai gaba ɗaya tare da tabbatar da cewa kamfanonin haƙar ma’adanai suna taimaka wa al’ummomin yankunan da suke aiki a cikinsu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Caleb Muftwang gwamna Haƙar Ma adanai matsalar tsaro haƙar ma adanai ayyukan haƙar
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
Gwamnatin mamayar Isra’ila ta yanke hukuncin kisa kan masu fama da cutar kansa da kuma waɗanda suke fama da matsalar koda na mutuwa a Gaza domin hana fitar da su wata kasa don neman magani
Cibiyar Kare Hakkin Dan Adam ta Gaza ta bayyana matukar damuwarta game da tabarbarewar lafiyar marasa lafiya da ke fama da cutar kansa da kuma cutar koda a Zirin Gaza. Wadannan cututtuka sun kara ta’azzara ne sakamakon hare-haren sojojin mamayar Isra’ila kan Gaza da kuma ci gaba da killace yankin bayan tsagaita bude wuta, gami da hana shigar dq magunguna da kayayyakin ayyukan likitanci masu muhimmanci cikin yankin. Cibiyar ta kuma yi nuni da tsauraran matakan fitar da marasa lafiya zuwa ƙasashen waje don neman magani.
A cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Lahadi, Cibiyar ta tabbatar da cewa, wannan yanayin ba shi da wata shakka cewa Isra’ila na aiwatar da manufar kisan gilla a kan dubban marasa lafiya ta hanyar hana su ‘yancinsu na rayuwa da magani da gangan, da kuma canza wahalarsu zuwa wani nau’in hukunci na gama gari.
Cibiyar ta ambaci majiyoyin lafiya da ke tabbatar da cewa, akwai marasa lafiya 12,500 da ke fama da cutar kansa a Zirin Gaza, ciki har da ƙananan yara. Ta lura cewa mata sun kai kusan kashi 52% na dukkan masu cutar kansa a Gaza.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kasar Qatar Ta Ba Da Tallafin Gaggawa Ga Al’ummar Sudan Bayan Gumurzun El-Fasher November 2, 2025 IAEA : Babu wata shaida da ke nuna cewa Iran na kera makaman nukiliya November 2, 2025 Amurka : zamu dauki matakin soja idan Najeriya ta gaza kawo karshen kashe Kiristoci November 2, 2025 Hamas ta musanta zargin Amurka na cewa tana sace kayan agaji a Gaza November 2, 2025 Wasu Yan Ta’adda Sun Kashe Dakarun Sa Kai 2 A Kudu Maso Gabashin Iran November 2, 2025 Sojojin Amurka Na Kara Fuskantar Venezuwela Adaidai Lokacin da Trump Ke Musanta Batun Kai Hari November 2, 2025 Isra’ila Ta Kashe Mutane 4 Tare Da Jikkata Wasu Guda 3 A Kudancin Labanon November 2, 2025 Iran Ta Gargadi Isra’ila Kuma Tasha Alwashin Kare Shirinta Na Nukiliya November 2, 2025 Shugaban AmurkaTrump ya yi barazanar daukar matakin soji kan Najeriya November 2, 2025 Kamaru: Jagroan ‘Yan Hamayya Ya Yi Kira Da A Tsayar Da Harkoki A Fadin kasar November 1, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci