Hukumar bayar da gudunmawar fansho ta Jihar Jigawa da Kananan Hukumomin jihar ta kulla yarjejeniyoyi da wasu mashahuran Hukumomin Asusun Fansho guda shida (PFA) da nufin tabbatar da tafiyar da kudaden fansho na jihar yadda ya kamata.

Shugaban ma’aikata na jiha Alhaji Muhammad K Dagaceri wanda ya jagoranci rattaba hannu kan yarjejeniyar a madadin gwamnatin jihar Jigawa a gidan fensho na Dutse ya ce taron yana kara jaddada kudirin gwamnati na  tabbatar da gaskiya da inganci a tsarin tafiyar da fansho.

Ya kuma jaddada mahimmancin kula da harkokin kudi da kuma bukatar samar wa wadanda suka yi ritaya kudaden fansho domin ci gaba da gudanar da rayuwarsu.

“Wannan yarjejeniya ta nuna wani gagarumin ci gaba a kokarin da muke yi na ganin cewa ma’aikatanmu da suka yi ritaya sun samu haƙƙinsu a kan lokaci.”

Alhaji Muhammad Dagaceri ya ci gaba da bayyana cewa, an zabo shugabannin asusun fansho ne ta hanyar tantancewa.

A cewarsa, masu gudanar da ayyukan za su samar da ingantattun ayyukan gudanarwa, da suka hada da dabarun saka hannun jari, da kula da ayyukan asusu da inganta ayyukan abokan ciniki.

Shugaban Ma’aikatan ya ce Hukumar Fansho ta Jihar Jigawa za ta sa ido a kan hadakar, tare da tabbatar da cewa PFA sun bi ka’ida da kuma cika alkawuran da suka dauka ga Jihar da masu karbar fansho.

Ya jaddada sadaukarwar gwamnatin Gwamna Umar Namadi wajen kyautata jin dadin ma’aikatan da suka yi ritaya, yana mai cewa wannan wani bangare ne na kokarin inganta ayyukan gwamnati da kuma kaucewa rikon sakainar kashi a harkokin tafiyar da dukiyar jihar.

Da yake jawabi a madadin  hukumomin na PFA Manajan Daraktan Asusun Fansho na Premium Hamisu Bala Idris, ya tabbatar wa hukumar cewa PFA  da aka zaba za su ci gaba da aiki yadda ya kamata ta hanyar bin duk wasu sharuddan da ke cikin yarjejeniyar.

Hamisu, ya bayyana tsarin fansho na jihar Jigawa a matsayin wanda ya fi kowanne a fadin kasar nan.

A nasa jawabin, Shugaban  Hukumar  Fansho ta Jihar Jigawa da Kananan Hukumomi, Dokta Bilyaminu Shitu Aminu ya bayyana cewa, zababbun  asusun fansho guda shida da za su kula da dukiyar hukumar su ne, Premium Pension Fund (Lead PFA), da PAL Pension, da GT Pension, da  NLPC Pension, da  Norrenberger Pension da Cruder.

Dakta Bilyaminu Shitu Aminu ya yabawa Gwamna Malam Umar  Namadi bisa gagarumin goyon bayan da ya bayar ga shirin da ya sa Jihar ta zama abin koyi a kasar nan.

Usman Muhammad Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa Yarjejeniya Jihar Jigawa jihar Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Araghchi : Za’ayi Tattaunawar Iran da Amurka ta gaba a Rome bayan taron E3

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya ce za a yi taro karo na hudu na shawarwari tsakanin Tehran da Washington kan shirin nukiliyar Jamhuriyar Musulunci ta Iran a birnin Rome na kasar Italiya a ranar Asabar mai zuwa.

M. Araghchi ya fadawa manema labarai a gefen taron majalisar ministocin gwamnatin kasar na mako-mako yau Laraba cewa, inda ya ce taron na Rome zai kasance gabanin wani taro a ranar Juma’a na tsakanin Tehran da kasashen Turan nan uku da ake wa lakabi da E3 wato – Ingila, Faransa da kuma Jamus wadanda suka sanya hannu kan yarjejeniyar nukiliyar Iran ta 2015.

Ya ce rawar da kasashen Turai uku ke takawa ta ragu sakamakon manufofinsu a tattaunawar da aka dade ana yi, don haka a shirye muke mu gudanar da zagaye na gaba na shawarwari da su a birnin Rome.

Babban jami’in diflomasiyyar ya kara da cewa, Tehran na da burin warware batun nukiliyarta cikin lumana.”

Da aka tambaye shi game da halin da ake ciki na baya-bayan nan na kudaden da Iran ta toshe saboda takunkumin da kasashen yamma suka kakaba mata, Araghchi ya ce daskararrun kudaden na daga cikin takunkumin da ya zama dole a dagewa iran.

Kawo yanzu Iran da Amurka sun yi tattaunawa har uku ta farko a Oman, ta biyu a Italiya sai kuma wace aka gudanar a ranar Asabar data gabata a Oman.

Dukkanin bangarorin na cewa akwai fata mai kyau a jerin tattaunawar da suka gabata.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwastam Ta Kama Jirage Marasa Matuka Da Sauran Kayayyaki Da Darajarsu Ta Haura Naira Biliyan 921 A Legas
  • Araghchi : Za’ayi Tattaunawar Iran da Amurka ta gaba a Rome bayan taron E3
  • Gwamnan Sokoto Ya Amince Da Sauya Wa Manyan Sakatarori 25 Ma’aikatu A Jihar 
  • Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Shirya Fara Tantance ‘Yan Fansho
  • Gwamna Namadi Ya Nada Aisha Mujaddadi Sabuwar Shugabar Hukumar InvestJigawa
  • Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok
  • Jihar Kebbi Ta Kammala Shirye-shiryen Aikin Hajjin 2025
  • Hajjin 2025: An Fara Yi Wa Maniyyata Allurar Rigakafi A Jigawa
  • Hajjin 2025: Gwamna Namadi Ya Nada Sarkin Kazaure Amirul Hajj
  • Al-Shara Ya Ki Abincikewa Da Tsarin Tarayya Wanda Kurdawan Kasar Siriya  Suke Bukata