Malamai Na Karbar Horo Akan Shirin Ilimin Mata Na AGILE a Jigawa
Published: 21st, February 2025 GMT
Shirin karfafa karatun mat (AGILE), ya fara horar da Malamai 20 na kwanaki 3 domin gudanar da shirin ba da ilimi na zamani mai suna dama ta biyu ta samun ilimi. “Second chance education bangaren” a Kano.
Shugabar Bangaren Aikin, Miss Hafsat Adhama, ta bayyana haka a wajen taron cin abincin rana da aka gudanar a Dutse, babban birnin jihar Jigawa.
Ta bayyana cewa, sama da malamai 300 ne suka gabatar da aikace-aikacen kuma an tantance su bisa la’akari da cancantarsu, da gogewa a fannin ilimin boko, fahimtar yanayin gida, da kuma sha’awar yara mata masu tasowa.
Ta yi nuni da cewa, tsarin ya ƙare ne a zaɓin ƙwararrun malamai 60, tare da tabbatar da cewa an zaɓi mafi kyawun kayan aiki da ma’aikata ne kawai don tallafawa shirin AGILE.
Miss Hafsat Adhama ta ce, wannan tsattsauran tsarin zaɓen, yana ƙara jaddada himmar shirin AGILE da abokan haɗin gwiwarsa, na samarwa ‘yan mata ilimi dama na biyu mai ma’ana don samun kyakkyawar makoma.
Ta kuma bayyana cewa, kimanin cibiyoyin koyo 60 ne aikin ya gano a wurare daban-daban a fadin kananan hukumomi 44 na jihar Kano. Don haka Hafsat ta umurci wadanda suka ci gajiyar shirin da su mai da hankali a lokutan horon
A nasa jawabin, mai ba da shawara kan harkokin fasaha na shirin Farfesa Auwal Halilu ya jaddada muhimmancin wannan horon, inda ya ce horo ne na musamman da ke bukatar maida hankali.
Ya kuma bukaci mahalarta taron da su kula domin akwai gibi mai yawa tsakanin ilimin boko.
Farfesa Halilu ya bukace su da su kasance masu sada zumunci da saukin kai, domin sanya ilimin da ake bukata a cikin zukatan daliban.
A yayin gabatar da nasa jawabin, kodinetan aikin, Alhaji Mujittapha Aminu ya ce, tantance cibiyoyin koyo ya ba da fifiko wajen samun dama, aminci da taimakon al’umma.
A cewarsa, samar da ababen more rayuwa don samar da yanayi mai kyau da kwanciyar hankali ga ‘yan mata masu tasowa, su ma abubuwan da aka yi la’akari da su wajen zabar wuraren koyo.
Ya kara da cewa, an gano sama da cibiyoyin koyo 100 a fadin kananan hukumomi 44, amma duk da haka an kammala tantance cibiyoyin koyo guda 20.
Alhaji Mujttapha ya jaddada cewa, za su tabbatar da cewa an zabo ma’aikata masu inganci don tallafawa shirin AGILE.
Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, Shirin Koyar da ’Yan Matan Matasa (AGILE) da ke Kano, wani muhimmin shiri ne da aka tsara don samarwa ‘yan mata masu tasowa damar samun ingantaccen ilimi na biyu ta hanyar guraben karatu na yau da kullun.
Shirin yana da nufin cike gibin ilimi ga ‘yan matan da ba sa zuwa makaranta, inganta daidaiton jinsi da karfafawa ‘yan mata matasa ilimi da dabarun rayuwa masu mahimmanci don ci gaban kansu da zamantakewa.
USMAN MZ
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Namadi Ya Nada Aisha Mujaddadi Sabuwar Shugabar Hukumar InvestJigawa
Gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Umar Namadi, ya amince da nadin Aisha Shehu Mujaddadi a matsayin shugabar Hukumar Kula da Zuba Jari ta Jihar Jigawa (InvestJigawa).
Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Sakataren Gwamnatin Jihar Jigawa, Malam Bala Ibrahim, ya fitar ga manema labarai.
Sanarwar ta ce “Aisha Mujaddadi ta samu digirinta na farko a fannin tattalin arziki a Jami’ar Maiduguri a shekarar 1996, ta kara inganta iliminta da samun digiri na biyu a fannin Gudanar da Kasuwanci (MBA) daga Jami’ar Bayero, Kano a shekarar 2011.“
Malam Bala Ibrahim ya bayyana cewa Aisha Mujaddadi ta samu gogewa na tsawon shekaru 19 a fannin aikin shawarwari na ci gaban kasa da kasa, inda ta yi aiki a kan muhimman ayyuka da shirye-shirye tare da Bankin Duniya, Ma’aikatar Harkokin Waje, Harkokin kungiyar kasashen renon Ingila da Ci Gaban Birtaniya (FCDO), da Tarayyar Turai (EU), wanda hakan ya bata kwarewar da ta dace da sabon mukaminta.
Ya kara da cewa, Aisha Mujaddadi ta kasance a cikin kwamitoci da dama a matakin jiha da na tarayya, kuma ta taba zama memba a kwamitin gudanarwa na Hukumar Tara Haraji ta Jihar Kaduna.
Sakataren Gwamnatin a jaddada cewa an yi nadin ne bisa cancanta, kwarewa da gaskiya, wanda ke nuna amincewar wannan gwamnati da kwarewar Aisha Mujaddadi.
Ya bayyana fatan cewa sabuwar Darakta Janar din za ta sauke nauyin da aka dora a kanta tare da kawo ci gaba mai ma’ana ga Jihar Jigawa.
Ya kara da cewa, nadin Aisha Shehu Mujaddadi a matsayin Darakta Janar na InvestJigawa ya fara aiki nan take.
Usman Muhammad Zaria