Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-11-03@09:26:31 GMT

Malamai Na Karbar Horo Akan Shirin Ilimin Mata Na AGILE a Jigawa

Published: 21st, February 2025 GMT

Malamai Na Karbar Horo Akan Shirin Ilimin Mata Na AGILE a Jigawa

Shirin karfafa karatun mat (AGILE), ya fara horar da Malamai 20 na kwanaki 3 domin gudanar da shirin ba da ilimi na zamani mai suna dama ta biyu ta samun ilimi. “Second chance education bangaren” a Kano.

Shugabar Bangaren Aikin, Miss Hafsat Adhama, ta bayyana haka a wajen taron cin abincin rana da aka gudanar a Dutse, babban birnin jihar Jigawa.

Ta bayyana cewa, sama da malamai 300 ne suka gabatar da aikace-aikacen kuma an tantance su bisa la’akari da cancantarsu, da gogewa a fannin ilimin boko, fahimtar yanayin gida, da kuma sha’awar yara mata masu tasowa.

Ta yi nuni da cewa, tsarin ya ƙare ne a zaɓin ƙwararrun malamai 60, tare da tabbatar da cewa an zaɓi mafi kyawun kayan aiki da ma’aikata ne kawai don tallafawa shirin AGILE.

Miss Hafsat Adhama ta ce, wannan tsattsauran tsarin zaɓen, yana ƙara jaddada himmar shirin AGILE da abokan haɗin gwiwarsa, na samarwa ‘yan mata ilimi dama na biyu mai ma’ana don samun kyakkyawar makoma.

Ta kuma bayyana cewa, kimanin cibiyoyin koyo 60 ne aikin ya gano a wurare daban-daban a fadin kananan hukumomi 44 na jihar Kano. Don haka Hafsat ta umurci wadanda suka ci gajiyar shirin da su mai da hankali a lokutan horon

A nasa jawabin, mai ba da shawara kan harkokin fasaha na shirin Farfesa Auwal Halilu ya jaddada muhimmancin wannan horon, inda ya ce horo ne na musamman da ke bukatar maida hankali.

Ya kuma bukaci mahalarta taron da su kula domin akwai gibi mai yawa tsakanin ilimin boko.

Farfesa Halilu ya bukace su da su kasance masu sada zumunci da saukin kai, domin sanya ilimin da ake bukata a cikin zukatan daliban.

A yayin gabatar da nasa jawabin, kodinetan aikin, Alhaji Mujittapha Aminu ya ce, tantance cibiyoyin koyo ya ba da fifiko wajen samun dama, aminci da taimakon al’umma.

A cewarsa, samar da ababen more rayuwa don samar da yanayi mai kyau da kwanciyar hankali ga ‘yan mata masu tasowa, su ma abubuwan da aka yi la’akari da su wajen zabar wuraren koyo.

Ya kara da cewa, an gano sama da cibiyoyin koyo 100 a fadin kananan hukumomi 44, amma duk da haka an kammala tantance cibiyoyin koyo guda 20.

Alhaji Mujttapha ya jaddada cewa, za su tabbatar da cewa an zabo ma’aikata masu inganci don tallafawa shirin AGILE.

Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, Shirin Koyar da ’Yan Matan Matasa (AGILE) da ke Kano, wani muhimmin shiri ne da aka tsara don samarwa ‘yan mata masu tasowa damar samun ingantaccen ilimi na biyu ta hanyar guraben karatu na yau da kullun.

Shirin yana da nufin cike gibin ilimi ga ‘yan matan da ba sa zuwa makaranta, inganta daidaiton jinsi da karfafawa ‘yan mata matasa ilimi da dabarun rayuwa masu mahimmanci don ci gaban kansu da zamantakewa.

USMAN MZ

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda

Daga Usman Muhammad Zaria

 

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta yi kira ga mazauna jihar Jigawa da su kasance masu bin doka da oda, tare da yin aiki kafada da kafada da rundunar ‘yan sanda domin tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali a fadin jihar.

Kwamishinan ‘Yan Sanda na jihar Jigawa, CP Dahiru Muhammad, ne ya bayyana haka lokacin da ya karɓi sabbin motoci 10 kirar Toyota Hilux da Gwamna Umar Namadi ya bai wa rundunar a Dutse, babban birnin jihar.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, SP Lawan Shiisu Adam, ya fitar, CP Dahiru Muhammad ya yaba da jajircewar Gwamna Umar Namadi wajen tallafa wa hukumomin tsaro domin sauke nauyin da ke kansu a jihar.

Ya bayyana cewa, wannan gudummawa ta nuna cikakken kudirin gwamnatin Gwamna Namadi na ƙara inganta harkokin tsaro da kuma tallafawa Rundunar ‘Yan Sanda ta Najeriya wajen aiwatar da aikinta na kare rayuka da dukiyoyin jama’a a fadin jihar.

Kwamishinan ya nuna cewa, waɗannan sabbin motoci 10 za su taimaka matuƙa wajen rage lokacin da ake ɗauka kafin amsa kiran gaggawa, tare da ƙara inganta aikin rundunar a fadin jihar.

Ya ƙara da cewa, za a yi amfani da motocin yadda ya kamata, tare da kula da su don tabbatar da ingantaccen  tsaro.

CP Dahiru Muhammad ya kuma sake jaddada aniyar rundunar wajen ci gaba da tabbatar da zaman lafiya, doka da oda, tare da ƙarfafa haɗin gwiwa da sauran hukumomin tsaro da masu ruwa da tsaki.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Trump ya jaddada shirin Amurka na kai hari a Najeriya
  • Hamas Ta yi Watsi Da Zargin Da Amurka Tayi Mata Kan Batun Motocin Agaji A Gaza
  • Ministar Jin Dadin Jama’a ta Sudan: Mayakan RSF Sun Kashe Mata 300 Da Yi Wa 25 Fyade A El Fasher
  • Gidauniyar IRM Da KADCHMA, Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna
  • Muna shirin kai farmaki a Nijeriya — Ma’aikatar Yaƙin Amurka
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Kwamitin Tsaron MDD ya goyi bayan shirin Morocco game da yankin Yammacin Sahara
  • Amurka Na Shirin Kai Hari Kan Kasar Venzuwela A Kowanne Lokaci Daga Yanzu
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
  • Manoma a Jigawa Sun Jinjinwa Kungiyar Sasakawa Africa Bisa Bada Tallafi a Harkar Noma