Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-08-02@00:44:48 GMT

Malamai Na Karbar Horo Akan Shirin Ilimin Mata Na AGILE a Jigawa

Published: 21st, February 2025 GMT

Malamai Na Karbar Horo Akan Shirin Ilimin Mata Na AGILE a Jigawa

Shirin karfafa karatun mat (AGILE), ya fara horar da Malamai 20 na kwanaki 3 domin gudanar da shirin ba da ilimi na zamani mai suna dama ta biyu ta samun ilimi. “Second chance education bangaren” a Kano.

Shugabar Bangaren Aikin, Miss Hafsat Adhama, ta bayyana haka a wajen taron cin abincin rana da aka gudanar a Dutse, babban birnin jihar Jigawa.

Ta bayyana cewa, sama da malamai 300 ne suka gabatar da aikace-aikacen kuma an tantance su bisa la’akari da cancantarsu, da gogewa a fannin ilimin boko, fahimtar yanayin gida, da kuma sha’awar yara mata masu tasowa.

Ta yi nuni da cewa, tsarin ya ƙare ne a zaɓin ƙwararrun malamai 60, tare da tabbatar da cewa an zaɓi mafi kyawun kayan aiki da ma’aikata ne kawai don tallafawa shirin AGILE.

Miss Hafsat Adhama ta ce, wannan tsattsauran tsarin zaɓen, yana ƙara jaddada himmar shirin AGILE da abokan haɗin gwiwarsa, na samarwa ‘yan mata ilimi dama na biyu mai ma’ana don samun kyakkyawar makoma.

Ta kuma bayyana cewa, kimanin cibiyoyin koyo 60 ne aikin ya gano a wurare daban-daban a fadin kananan hukumomi 44 na jihar Kano. Don haka Hafsat ta umurci wadanda suka ci gajiyar shirin da su mai da hankali a lokutan horon

A nasa jawabin, mai ba da shawara kan harkokin fasaha na shirin Farfesa Auwal Halilu ya jaddada muhimmancin wannan horon, inda ya ce horo ne na musamman da ke bukatar maida hankali.

Ya kuma bukaci mahalarta taron da su kula domin akwai gibi mai yawa tsakanin ilimin boko.

Farfesa Halilu ya bukace su da su kasance masu sada zumunci da saukin kai, domin sanya ilimin da ake bukata a cikin zukatan daliban.

A yayin gabatar da nasa jawabin, kodinetan aikin, Alhaji Mujittapha Aminu ya ce, tantance cibiyoyin koyo ya ba da fifiko wajen samun dama, aminci da taimakon al’umma.

A cewarsa, samar da ababen more rayuwa don samar da yanayi mai kyau da kwanciyar hankali ga ‘yan mata masu tasowa, su ma abubuwan da aka yi la’akari da su wajen zabar wuraren koyo.

Ya kara da cewa, an gano sama da cibiyoyin koyo 100 a fadin kananan hukumomi 44, amma duk da haka an kammala tantance cibiyoyin koyo guda 20.

Alhaji Mujttapha ya jaddada cewa, za su tabbatar da cewa an zabo ma’aikata masu inganci don tallafawa shirin AGILE.

Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, Shirin Koyar da ’Yan Matan Matasa (AGILE) da ke Kano, wani muhimmin shiri ne da aka tsara don samarwa ‘yan mata masu tasowa damar samun ingantaccen ilimi na biyu ta hanyar guraben karatu na yau da kullun.

Shirin yana da nufin cike gibin ilimi ga ‘yan matan da ba sa zuwa makaranta, inganta daidaiton jinsi da karfafawa ‘yan mata matasa ilimi da dabarun rayuwa masu mahimmanci don ci gaban kansu da zamantakewa.

USMAN MZ

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Qolibaf: Barin HKI Ta Yi Abinda Taga Dama Ne Yana Karfafa Mata Giwa

Kakakin majalisar dokokin kasar Iran Mohammad Baqir Qalibaf ya bayyana cewa kyale HKI wanda kasashen duniya suka yi ne, ya ke bawa HKI karfin giwan ci gaba da abinda take yi a gaza.

Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kakakin majalisar dokokin kasar ta Iran yana fadar haka a taron shuwagabannin majalisun dokokin wanda ake gudanarwa a halin yanzu a birnin Geneva.

Wannan dai shi ne taron shuwagabannin majalusun dokoki na duniya karo na 6 wanda MDD take daukar nauyinta.

Dangane da hare-haren da HKI da Amurka suka kaiwa kasar Iran a cikin watan Yunin da ya gabata kuma ,Qalibof ya bayyana cewa manufarsu it ce lalata shirin Nukliyar kasar Iran ta zaman lafiya, kwata-kwata. Alhali hukumar makamashin Nukliya ta duniya wato IAEA tana sanya iado a kan ayyukan sarrafa uranium da kasar take yi.

Shugaban majalisar dokokin kasar Iran ya bayyana cewa hare-haren kwanaki 12 wanda wadan nan kasashe biyu wadanda basa son zaman lafiya a Iran sun kai mutane kimani 1100 ga shahada. Sannan sun sanya shirin nukliyar kasar Iran cikin hatsari, wanda ya tilasta mana daukar matakai don kare shi.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Yunwa Ta Kashe Karin Falasdinawa 7 A Gaza July 30, 2025 Malta Zata Amince da Samuwar Falasdinu a Cikin Watan Satumba Mai Zuwa July 30, 2025 Amurka Ta Ce HKI Ba Zata Fice Daga Kasar Lebanon Ba Sai An Kwance Damarar Hizbullah July 30, 2025 Siriya Da HKI Zasu Gudanar Da Taro A Baku July 30, 2025  Girgizar Kasa Mai Karfi Ta Kada Yankin Kamtashatka Na Kasar Rasha July 30, 2025  Yahudawa ‘Yan Share Wuri Zauna Sun Kutsa Cikin Masallacin Kudus July 30, 2025 Kasashen Yankin Caribbean Suna Son Bunkasa Alakarsu Ta Kasuwanci Da Nahiyar Afirka July 30, 2025 Shugaban Kasar Ivory Coast Ya Bayyana Shirinsa Na Sake Tsayawa Takarar Shugabanci Karo Na Hudu July 30, 2025 Kasashen Iran Da Rasha Sun Tattauna Batun Hadin Gwiwar Kafofin Watsa Labarai A Tsakaninsu July 30, 2025 MDD Zata Aiwatar Da Hanyar Warware Rikicin Falasdinawa Da Yahudawan Sahayoniyya July 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Shirya Taron Bita Ga Kansiloli
  • Afirka ta Kudu na shirin daukar matakan kauce wa tasirin harajin Amurka
  • Habasha Ta Kaddamar Da Shirin Shuka Bishiyoyi Miliyan 700 A Rana Daya
  • An Horas Da Mata 600 Kan Abincin Yara Mai Gina Jiki A Jigawa
  • Gwamnatin Jigawa ta horas da malamai 20,000 fasahar sadarwar zamani
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Yi Allah Wadai Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Mata
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar da Tallafin Miliyoyin Naira Ga Ƴan NURTW da Mahauta a Jigawa
  • Qolibaf: Barin HKI Ta Yi Abinda Taga Dama Ne Yana Karfafa Mata Giwa
  • Majalisa ta ba NNPCL mako uku ya yi mata bayanin inda tirilyan 210 ta shiga
  • An Kaddamar da Makon MNCH na 2025, Ya Rarraba Fakitin Bayarwa 6,000, Kayan C/S 500