Jihar Kano Ta Samar Da Wani Salo Na Bunkasa Ilmin Addinin Musulunci A Jihar
Published: 21st, February 2025 GMT
Gwamnatin jihar Kano ta dauki wani gagarumin mataki na bunkasa ilimin addinin musulunci a jihar ta hanyar hada hannu da kungiyar Agaji ta Musulunci da ke Birtaniya, wato Muslim Charity For United Kingdom a turance.
Wannan haɗin gwiwar na nufin tallafa wa makarantun Islamiyya da kayayyakin koyon ilimi na zamani, da sauransu.
A cewar daraktan wayar da kan jama’a na ma’aikatar ilimi ta jihar Kano, Balarabe Abdullahi Kiru, wannan shiri ya yi daidai da kokarin da gwamnati ke yi na karfafa fannin ilimi.
Haɗin gwiwar zai magance matsalolin da ke addabar ilimin addinin Islama, da tabbatar da cewa makarantun Islamiyya sun sami tallafin da ya dace don samu ingantaccen yanayin karatu da koyarwa.
Ya yi nuni da cewa, Kwamishinan Ilimi na Jihar, Dakta Ali Haruna Makoda, ya bayyana fatan cewa, wannan hadin gwiwa zai inganta ilimin addinin Musulunci, musamman a tsarin makarantun Islamiyya.
Ya ce, shirin zai mayar da hankali ne wajen samar da kayayyakin koyo na zamani domin inganta kwazon dalibai.
Da take jawabi a madadin tawagar, shugabar kungiyar agaji ta addininMusuluncida ke Birtaniya, Dr. Samira Abubakar Abdullahi, ta bayyana cewa kungiyar na aiki tukuru a Najeriya domin tallafawa harkokin ilimi da kiwon lafiya.
Ta bayyana cewa gudummawar da suke bayarwa sun hada da shirye-shiryen gyara makarantu, ayyukan ci gaban ilimi, da ayyukan kiwon lafiya.
“Mun zo ma’aikatar don tattaunawa kan bangarorin haɗin gwiwa da kuma yi wa kwamishina bayani game da ayyukanmu,” inji ta.
Kungiyar agajin tana aiki tukuru a Najeriya don tallafawa ayyukan ilimi da kiwon lafiya.
Daga Khadija Aliyu
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Kungiyar Agaji
এছাড়াও পড়ুন:
Manyan Malaman Roman Katolika Sun Fara Taron Zabar Paparoma
Manyan malaman addinin darikar Roman Katolika za su fara Shirin zabar shugaban darikar tasu a fadar Vatican
Adadin manyan malaman addinin masu mukamin “Cardinal” 130 ne za su taru a fadar Vatican, domin su zabi wanda zai maye gurbin Paparoma Farancis da ya rasu.
Sai dai masu kusancin da fadar ta Vatican suna bayyana cewa, da akwai batutuwa da dama da su ka raba kawunan manyan malaman addinin na Roman Katolika da su ka batun auren jinsi, da rawar da mata za su taka a karkashin inuwar cocin.
Sai dai kuma wani mai sharhi akan abubuwan da su ka shafi cocin, Reese ya bayyana cewa, masu zaben za su mayar da hankali ne akan wanda zai kare ayyukan da mamacin Paparoma Francis ya bari.
Tare da cewa babu kafa ta yin yakin neman zabe a tsakanin masu mukamin na Cardinal, sai dai da akwai wasu siffofi da halaye da ake son gani da wadanda za su iya zama ‘yan takara.
Ana sanar da wanda ya zama sabon Paparoma ne ta hanyar samun kaso 2/3 na kuri’un da manyan masu zaben su ka kada.
A bisa ka’idar cocin, duk wanda aka yi wa wankan tsarki na ” Baptisma”zai iya zama paparoma,amma kuma tun daga 1378 ba a zabi wanda bai kai mukamin “Cardinal” ba.