Gwamna Umar Namadi  ya kaddamar da aikin gina titin Kanya Babba (Kwanar Duzau) zuwa Kankare zuwa Ballada zuwa Duzau zuwa Danhill zuwa Kyambo zuwa Mundu zuwa Goron Maje.

Aikin wanda aka bayar da shi kan kudi naira biliyan 6 da miliyan 300, wani muhimmin mataki ne a yunkurin gwamnatin jihar na inganta ababen more rayuwa da  hanyoyin sada yankuna.

Da yake jawabi a wajen taron, Gwamna Namadi ya jaddada muhimmancin hanyoyin, wajen samar da ci gaban tattalin arziki, da inganta hanyoyin samar da ababen more rayuwa, da inganta rayuwar al’ummar yankin.

Ya sake jaddada kudurin gwamnatinsa na samar da ingantattun ababen more rayuwa da za a dade ana amfana da su.

Ya kuma bayyana cewa,  ana sa ran  da zarar an kammala  aikin zai bunkasa kasuwanci, da saukaka kalubalen sufuri, da bude sabbin hanyoyin tattalin arziki ga mazauna yankin.

Malam Umar Namadi ya ce, gwamnatin jihar ta bayar da kwangilar gina sabbin hanyoyi arba’in da bakwai na tsawon sama da kilomita dari tara a jihar.

Ya bayyana cewa ana ci gaba da gudanar da ayyuka a dukkan hanyoyin da aka bayar da aikinsu.

A nasa jawabin kwamishinan ayyuka da sufuri na jihar Injiniya Gambo S Malam ya ce an bayar da aikin gina hanyar kanya Babba, zuwa Duzau zuwa Goron Maje akan kudi sama da naira biliyan shida.

Wakilinmu ya ruwaito cewa, Karamar Ministar Ilimi Farfesa Suwaiba Ahmed Babura ce ta kaddamar da aikin.

Wasu daga cikin manyan baki da suka halarci bikin sun hada da, mataimakin gwamnan jihar Jigawa Injiniya Aminu Usman, da kakakin majalisar dokokin jihar Alhaji Haruna Aliyu Dangyatum da sakataren gwamnatin jihar Malam Bala Ibrahim da dai sauransu.

Usman Muhammad Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisa ta amince Tinubu ya karɓo rancen dala biliyan 2.35

Majalisar Tarayya, ta amince da buƙatar Shugaba Bola Ahmed Tinubu na karɓo rancen dala biliyan 2.35 domin cike giɓin kasafin kuɗin shekarar 2025.

Dukkanin Mjalisun sun amince da buƙatar ne a ranar Laraba, bayan sun duba rahoton kwamitin karɓar basussuka na cikin gida da na waje.

Zargin Kisan Kiristoci: ’Yan majalisar Amurka sun yi amfani da bayanai marasa tushe — Gwamnati ACF ta mara wa gwamnatin Tinubu baya

Haka kuma, majalisar ta amince da buƙatar Tinubu na fitar da dala miliyan 500 domin samar da muhimman ayyuka kamar faɗaɗa hanyoyin samun kuɗi ga ƙasar nan.

A cikin wasiƙar da ya aike wa majalisar tun a farkon watan nan, Shugaba Tinubu, ya bayyana cewa neman rancen ya zama dole domin aiwatar da kasafin kuɗin 2025.

Kasafin wanda ya ƙunshi Naira tiriliyan 9.28 na nufin cike giɓin da ake da shi a kasafin 2025.

Ya ce hakan zai taimaka wajen kauce wa kasa biyan bashi da kuma bin inganta ƙa’idojin kasuwar hada-hadar bashi ta duniya.

“Jimillar kuɗin da za a nema daga waje; dala biliyan 1.229 na sabon rance da dala biliyan 1.118 na sake biyan tsohon bashi zai kai dala biliyan 2.347,” in ji wasiƙar.

’Yan majalisa sun bayyana cewa rancen zai taimaka wa gwamnati ci gaba da aiwatar da muhimman ayyukan raya ƙasa da kuma daidaita tattalin arziƙi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 
  • Borno ta fara fitar da kayan robobi zuwa ƙasashen waje – Zulum
  • Gwamnatin Gombe ta saurari ra’ayoyin jama’a kan kasafin kuɗin 2026
  • Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai
  • Jihar Jigawa Ce Ta Fara Biyan Kudaden Kujerun Aikin Hajjin 2026- NAHCON
  • Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya
  • Majalisa ta amince Tinubu ya karɓo rancen dala biliyan 2.35