Yadda na yi wa budurwar da muka haɗu a Facebook gunduwa-gunduwa —Matashi
Published: 17th, February 2025 GMT
Wani matashi da aka kama kan yin gunduwa-gunduwa da budurwarsa da suka haɗu a Facebook bayan ta je ɗakinsa ya bayyana dalilinsa na aikata hakan.
Matashin mai shekaru 29 da ke iƙirarin malumtar addini ya amsa a wurin ’yan sanda masu bincike cewa shi ne ya yi wa gawar budurwar tasa gunduwa-gunduwa.
Ya shaida musu cewa a Facebook ya haɗu da ita, inda daga bisani ta ziyarci ɗakinsa a unguwar Olunlade a garin Ilori, bayan ta je wani biki.
Sai dai ya musanta zargin da ake masa na kashe ɗalibar mai suna Hafsah Yetunde Bello domin yin tsafi.
Jirgin soji ya kashe fararen hula a Katsina Malaman addini sun yi wa ’yan siyasa juyin mulki —Sule Lamiɗo Ku tona asirin ’yan tsubbu —Sarkin Ilori ga malaman addiniA cikin bidiyon tambayoyin da ’yan sanda ke wa matashin mai suna Abdulraham Bello, ya ce bayan zuwan budurwar tasa ne ya je ya sayo mata abinci, bayan ta bayyana masa cewa tana jin yunwa.
Ya shaida wa masu binciken nasa cewa bayan ya dawo daga sayo abincin ne ya iske ta tana shassheka a ɗakin.
“Ba a jima ba sai ta mutu. Ni kuma na tsotsa, babu wanda zan iya zuwa gaya wa ya taimaka min, shi ne ne sassara gawarta na yi mata gunduwa-gunduwa na je na jefar a wata bola a unguwar.
“A rikice nake, ban san abin da zan yi ba, ko tunanin wata hanya ta daban. Amma ban taɓa yin haka ba, wannan ne karon farko,” in ji matashin a ofishin ’yan sanda.
A cikin bidiyon da ya yi jawabin nasa cikin harshen Yarbanci ya bayyana cewa a halin yanzu yana neman gurbin karatu ne a Jami’ar Jihar Kwara (KWASU), Malete.
Mamaciyar dai ɗalibar aikin ƙarshe ce a Kwalejin Koyarwa ta Jihar Kwara.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: gunduwa gunduwa gunduwa gunduwa
এছাড়াও পড়ুন:
An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
Hukumomin ’yan sandan Najeriya tare da haɗin gwiwar wasu hukumomin tsaro sun samu gagarumar nasara a ƙoƙarin da suke na daƙile munanan laifuka a ƙasar.
Na baya-bayan nan dai shi ne ceto mutanen da aka sace, da kashe wasu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne da kuma ƙwato manyan bindigogi da alburusai a jihohin Delta da Katsina.
Mulkin Tinubu ya fi kowane muni tun bayan dawowar mulkin farar hula — Dalung An kama ’yar Najeriya da laifin safarar ɗalibai 15 a AustraliaA wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan, Olumuyiwa Adejobi ya fitar, ya ce a jihar Katsina an samu gagarumar nasara a ranar 8 ga watan Yunin 2025, inda haɗin gwiwar JTF da suka haɗa da jami’an ’yan sanda da sauran jami’an tsaro suka daƙile wani yunƙurin yin garkuwa da mutane a hanyar ƙauyen Danmusa zuwa Mara Dangeza a ƙaramar hukumar Danmusa.
Adejobi ya ce hakan na iya yiwuwa ne ta hanyar shigar da wasu gungun ’yan bindiga da suka yi yunƙurin guduwa da waɗanda aka yi garkuwa da su a wani artabu da ya kai ga ceto mutum 11.
Nasarar da aka samu yankin Kudu maso KuduA halin da ake ciki kuma, a yankin Kudu maso Kudu, Jihar Delta, hukumar ’yan sanda ta kama wani Abubakar Hassan, wanda babban wanda ake zargi da aikata laifin satar mutane ne a tsakanin jihohin Delta da Ribas da Imo, da Enugu.
Jami’an da ke da alaƙa da samun nasarar sun yi hakan ne yayin da suke aiki da sahihan bayanai.
A yayin da ake yi masa tambayoyi, Hassan ya bayyana cewa shi ne ya jagoranci gudanar da hari a yankin Ughelli-Ozoro na jihar mai arzikin man fetur.
Ya kuma jagoranci jami’an ’yan sanda zuwa maɓoyarsa a wani daji da ke Ozoro. A can jami’an sun ƙwato bindigogi ƙirar AK-47 guda biyu da tarin alburusai huɗu da harsashi guda talatin da biyu.