Sheik Na’im Kassim: Babu Dalilin Ci Gaba Da Zaman Sojojin Mamaya A Lebanon
Published: 17th, February 2025 GMT
Babban sakataren kungiyar Hizbullah ta kasar Lebanon Sheikh Na’im Kassim ya gabatar da jawabi da marecen jiya Lahadi inda ya tabo muhimman batutuwa da su ka shafi kasar ta Lebanon da kuma yammacin Asiya.
Sheikh Na’im Kassim ya ce wajibi ne ‘yan sahayoniya su janye sojojinsu daga kudancin kasar ta Lebanon domin babu wani dalili na cigaba da zamansu.
Shekih Na’im Kassim ya bayyana ranar 23 ga watan nan na Febrairu ta jana’izar Shahid Sayyid Hassan da kuma shahid Hashim Safiyuddin a matsayin ranar jaddada mubaya’a ga tafarkin da ya tafiyar da rayuwarsa a kansa da shi ne gwgawarmaya.
Babban makatakardar kungiyar ta Hizbullah dai ya gabatar da jawabi ne na tunawa da jagororin Hizbullah da su ka gabata, inda ya yi kira da al’ummar kasar da su fito domin halartar jana’izar Shahid Sayyid Hassan Nasrallah.
Sheikh Na’im Kassim ya ce; Ina yin kira ga al’ummarmu da su fito sosai domin halartar jana’izar shahidai, Sayyid Hassan Nasrallah da kuma Shahid Sayyid Hashim.”
Babban magatakardar kungiyar ta Hizbullah ya kuma bayyana cewa duk wanda yake son yin matsin lamba akan Hizbullah domin ya raunanata, to ya kwana da sanin cewa ba zai sami nasarar yin hakan ba.
Dangane da batun hana jirgin saman Iran sauka a filin saukar jiragen sama na Beirut, saboda barazanar HKI, babban magatakardar kungiyar ta Hizbullah ya kirayi gwamnatin kasar ta Lebanon da ta sauya matsayar da ta dauka.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Na im Kassim ya
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar
Shugaba Xi ya kara da cewa, a halin da ake ciki yanzu, duniya na fuskantar sauye-sauye irin wadanda ba a taba gani ba kuma cikin sauri. Don haka, kamata ya yi kasashen biyu masu dadaddun wayewar kai su zurfafa koyi da juna, da shigar da sabon kuzari cikin gina cikakken salon hadin kai, bisa manyan tsare-tsare tsakaninsu, kana su tattaro karfin wayewar kai don gina al’umma mai makomar bai daya ga dukkanin bil’adama.
A wani ci gaban kuma, wakilin musamman na shugaban kasar Sin Xi Jinping wato ministan raya al’adu da yawon bude ido na kasar Sun Yeli, ya halarci bikin bude babban gidan adana kayan tarihin na GEM bisa gayyatar gwamnatin Masar. Kafin bikin, shugaba al-Sisi ya gana tare da gudanar da gajeriyar tattaunawa da Sun Yeli. (Saminu Alhassan)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA