Al’ummar Gundumar Kano Ta Arewa Sun Dara Bayan Kwashe Shekaru 10 Ba Ruwan Sha
Published: 17th, February 2025 GMT
An samar da ruwan sha a yankunan Danbatta, da Makoda da Minjibir dake gundumar Kano ta Arewa bayan kwashe kimanin shekaru goma.
Kwamishinan albarkatun ruwa na jihar Alhaji Umar Haruna Doguwa ya bayyana haka a wani rangadin da ya kai kananan hukumomin uku domin tantance yadda ake samar da ruwan sha ga al’umma.
Umar Doguwa ya bayyana cewa gwamna Abba Kabir Yusuf ya himmatu sosai wajen samar da ruwan sha a dukkan lungu da sako na jihar Kano.
Ya ce an gyara kananan cibiyoyin samar da ruwan sha a yankunan inda ake samar da ruwa babu kakkautawa.
Kwamishinan ya ce yanzu haka ana samun ruwan sha a kauyukan kunya, da Kilawa da ,wailare duk a karamar hukumar Minjibir yayin da ake kokarin ganin an samar da ruwan sha na karamar hukumar Danbatta.
“Abin takaici ne matuka, duk wadannan kauyukan sun shafe sama da shekaru takwas babu ruwa, duk da cewa suna da cibiyoyin samar da ruwan“.
Ya ce a halin yanzu ana ci gaba da gudanar da bincike a wadannan kauyukan domin tabbatar da cewa an gyara dukkan bututun da a halin yanzu wasu sun yi tsatsa da sauran matsaloli sakamakon rashin amfani da su na tsawon shekaru.
Doguwa ya kara da cewa, hakan na nuni da kokarin gwamna Abba Kabir Yusuf na farfado da samar da tsaftataccen ruwan sha ga al’ummar jihar.
Umar Haruna Doguwa ya ci gaba da cewa gwamnati ba za ta ragawa duk wanda aka samu yana karkatar da ruwan da aka tanadar don sha da amfanin gida ba zuwa gonaki don noman rani.
Abdullahi Jalaluddeen
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Ruwan Sha samar da ruwan sha ruwan sha a
এছাড়াও পড়ুন:
Tsoffin ma’aikatan NECO na neman a biya su bashin haƙƙoƙinsu
Tsoffin ma’aikatan Hukumar Shirya Jarabawar (NECO), da suka yi ritaya na neman a biya su haƙƙoƙinsu da suke bin bashi.
Shugaban ƙungiyar tsofffin ma’aikatan, Dokta Abdullahi Rotimi Williams ne ya bayyana hakan a bikin ƙaddamar da hedikwatar kungiyar a Minna, babban birnin Neja.
Dokta Bashir ya zama shugaban Majalisar Shari’ar Musulunci ta Nijeriya Dokta Bashir ya zama shugaban Majalisar Shari’ar Musulunci ta NijeriyaShugaban ya kuma koka kan yadda gwamnatin Nijeriya ta maida ritaya abin fargaba a wurin ma’aikata saboda tarin ƙalubalen da ke biyo bayan hakan, musamman maƙalewar haƙƙoƙinsu.
“Da yawa tsoron ritaya ake yi yanzu. Don haka wannan ƙungiyar za ta taimaka wajen rage waɗannan matsalolin.
“Babban ƙalubalen da muke fuskanta shi ne na lafiya. Don haka ina roƙon shugaban hukumar da ya tabbatar cewa daga yanzu an kammala shirye-shiryen da suka kamata kafin ma’aikacin NECO ya yi ritaya.”
Ya kuma ce duk da jagororin hukumar na yanzu sun biya wasu daga cikin haƙƙoƙin nasu, ba a kai ga biyan alawus ɗin ƙarin girma ba, da na tafiye-tafiye ba.