Kwara Ta Ware Naira Miliyan Dubu Biyar Don Kula Da Cibiyoyin Lafiyar Jihar
Published: 14th, February 2025 GMT
Gwamnatin jihar Kwara ta ware naira biliyan 5 domin inganta cibiyoyin kiwon lafiya a matakin farko guda 70 a kananan hukumomin uku na jihar.
Babban Sakatariyar Hukumar Kula da Lafiya a matakin farko ta Jihar Kwara (KWHCDA), Farfesa Nusirat Elelu ce ta bayyana haka a lokacin rattaba hannu kan kwangilolin da aka yi a hedikwatar Hukumar da ke Ilorin.
Ta ce matakin zai hada da inganta ababen more rayuwa, samar da lantarki ta amafani da hasken rana, da samar da wuraren zama na ma’aikata, da samar da ruwan sha da samar da kayan aikin asibiti na zamani a duk wuraren da ke amfana da cibiyoyin kiwon lafiya na farko.
Farfesa Elelu ya bayyana cewa shiga tsakani na zuwa ne tare da tallafin da Bankin Duniya ke tallafawa.
Ta yi nuni da cewa shirin zai sa cibiyoyin kula da lafiya matakin farko su kasance masu inganci don samar da ingantattun ayyukan kiwon lafiya a matakin farko a fadin jihar.
Kwamishinan ya ce gaba daya makasudin shi ne a mayar da dukkan cibiyoyin PHC ‘daidai da manufa’ tunda tsarin PHC shi ne farkon tuntuɓar tsarin kiwon lafiyar ƙasa.
Farfesa Elelu ya roki duk wadanda suka yi nasara da su tabbatar sun samar da ingantattun ayyuka don tabbatar da amanar da aka ba su.
A nasa bangaren manajan shirin na IMPACT, Dr. Michael Oguntoye, ya ce za a bayar da kwangilar ne cikin watanni 3 kuma jihar ba za ta lamunci tsaikon wajen aiwatar da aikin ba.
Dr.Oguntoye ya kara da cewa wadanda suka fara cin gajiyar shirin na IMPACT su ne yara da mata ‘yan kasa da shekaru biyar, inda ya ce aikin zai kuma inganta samar da ayyukan kiwon lafiya ga daukacin mazauna jihar.
Cov/Ali Muhammad Rabiu/Wababe
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Gyara Kwara Lafiya a matakin farko kiwon lafiya
এছাড়াও পড়ুন:
ALGON ta karrama Gwamna Buni da lambar yabo kan kawo ci gaba a Yobe
Ƙungiyar shugabannin ƙananan hukumomin Jihar Yobe (ALGON) ta karrama Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni, da lambar yabo ta karramawa bisa himmar ayyukan raya ƙasa da gwamnatinsa ke gudanarwa a faɗin jihar.
Karramawar, wacce aka bayyana a matsayin irinta ta farko a tarihin Jihar Yobe, shugabannin ƙananan hukumomi 17 na jihar suka ba da ita ga gwamna.
Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a BornoDa yake jawabi, shugaban ƙungiyar ALGON a Jihar Yobe, kuma shugaban ƙaramar hukumar Damaturu, Alhaji Bukar Adamu, ya yaba da yadda Gwamna Buni yake gudanar da harkokin mulki na bai ɗaya. Ya ce nasarorin da aka samu sun haɗa da fannoni na ilimi, noma, kiwon lafiya, kasuwanci, da samar da ababen more rayuwa.
“Babu wani sashe a jihar da aka bari a baya a cikin ayyukan ci gaban da Gwamna Mai Mala Buni ke aiwatarwa,” in ji Adamu.
A nasa martanin, Gwamna Buni, wanda mataimakinsa, Alhaji Idi Barde Gubana, ya wakilta, ya karɓi karramawar a matsayin “hanyar mayar da martani mai ƙarfi” da ke tabbatar da tasirin gwamnatinsa a matakin farko.
Ya kuma yi alƙawarin ci gaba da ƙoƙarin kai Yobe matsayin jiha da za ta iya gogayya da takwarorinta a fagen ci gaban ƙasa.
Wakilinmu ya ruwaito cewa taron ya samu halartar manyan jami’an gwamnati, ’yan siyasa daga ciki da wajen jihar, da kuma sarakunan gargajiya.