Gwamnatin jihar Kano, KNSG, ta ce ta tanadi hanyoyin dakile mace-macen mata masu juna biyu maimakon rage yawan mace-macen.

 

Kwamishinan lafiya na jihar Dr Abubakar Labaran Yusuf ne ya bayyana haka a lokacin da yake jawabi a wajen taron hadin gwiwa na Partners Coordination Forum (PCF) da aka gudanar a Kano.

 

A wata sanarwa mai dauke da sa hannun jami’in hulda da jama’a na ma’aikatar lafiya ta jihar Kano Ibrahim Abdullahi, ta bayyana cewa, Dakta Abubakar Labaran ya bayyana cewa gwamnati ta himmatu sosai wajen kawo sauyi a fannin kiwon lafiya a karkashin gwamnatin Gwamna Abba Kabir Yusuf, da niyyar ganin ba macen da ta mutu a lokacin haihuwa.

 

Ya yi karin haske kan gyare-gyaren da aka yi a cibiyoyin kula da lafiya na sakandare da kuma bayar da kwangiloli na inganta cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko sama da 200 a wani bangare na dabarun karfafa kiwon lafiyar mata masu juna biyu.

 

Ya nuna damuwarsa kan alkaluman da ke nuna cewa sama da kashi 70% na mata a Kano sun fi son haihuwa a gida da taimakon masu haihuwa na gargajiya maimakon neman magani a asibitoci.

 

Ya danganta hakan da rashin kwarin gwiwa kan ayyukan kiwon lafiya.

 

“Mata da yawa sun yi imanin cewa haihuwa a dakunan aurensu ya fi zuwa asibiti lafiya saboda sun daina amincewa da samun kulawar da ta dace. Don haka ne muke gyara asibitocinmu tare da karfafa cibiyoyin kula da lafiya a matakin farko. Manufarmu ita ce a samar da akalla cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko guda daya a kowace Unguwa ta Jihar Kano.”

 

An kammala taron tare da abokan hadin gwiwa da suka yi alkawarin bayar da goyon bayansu ga kokarin jihar Kano wajen cimma wannan gagarumin buri.

 

Khadijah Aliyu/Wababe

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Haihuwa Lafiya kiwon lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

Muhimmanci, Tasiri Da Kuma Amfanin Jigida Ga Mata

Ita jigida irin ta da ba haka kawai ake sakata ba, domin shahararru kuma jarumai ne a wacan lokacin suke yin ta don haka ne take da tasiri da kuma tsada ga masu saye.

Sai dai a baya akwai jigida ta ‘yan mata akwai ta matan aure da kuma na tsofaffi, kuma a wannan lokacin babu matsala ko wani gani-gani da ake yi wa macen da aka ganta sanye da jigida saboda abu ne da aka dauka na al’ada maimakon ado ko kiran maza da wasu ke ganin matan yanzu suke yi da jigida ba.

Yanzu dai sanya jigida ga mata ya bunkasa ya fadada har cikin kashen Turai. Matan turawa kamar yadda bincike ya tabbatar kashi 60 cikin 100 suna sawa.

Sai dai a wannan zamanin da muke ciki sanya jigida ga mata ya zama abin ado ne ba domin dalilai irin na camfi da muka ambata a baya da mutanen baya suke yi ba, duk da yake ana samun kadan daga cikin matan kauyawa masu saka jigida da manufa ta camfi.

Shima dai kamar irin na da ne, wannan zamanin ana yin jigida ne da wasu duwatsu masu kyalli da kuma robobi masu sheki wadanda nauyinsu bai kai irin na zamanin baya ba.

Babban alfanun da jigida yake yi wa mata kamar yadda bincike ya tabbatar a wannan lokacin shi ne, yana kara wa mace fadin kugunta ga irin matan nan da suke da karancisa.

Maza da dama da aka zanta da su sun nuna sha’awarsu ta ganin matansu na aure suna saka jigida domin yana karamusu kyau musamman idan mace tana sanye da kayan da za su bayyanasu.

Har ilayau cikin alfanun da jigida ke da shi shi ne ta kan motsa sha’awan maza a yayin da suka ji sautinsa ko suka hango shatinsa.

Sai dai duk da wadannan tasiri, mahimanci da alfanun da jigida ke da su ba duka mata bane suke sanyawa ba, haka ma maza da dama ba su son ganin mace da jigida. Wasu mutane sun riga sun kudura cewa duk mace ko budurwar da aka ga tana sa jigida ko aka ji sautinsa a tare da ita suna daukan irin wadannan matan mazinata ne.

Sannan kuma yanzu ana jigida ta mganin mata. Masu maganin mata sun samo yadda ake jigida da garin magani a maimakon duwatsun da ake yi da shi, sai a yi da maganin a ciccura ta kamar dutse sai a huda tsakiyar asa zare duk haka za’a jera su. Mata su daurashi a kugunsu yana maganin mata.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Masu ƙwacen waya sun kashe ma’aikacin Jami’ar Northwest a Kano
  • Martanin Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Kan Ta’addancin ‘Yan Sahayoniyya ya Shiga Rana Ta Biyu
  • Dakarun Kare Juyin Juya Halin Musulunci Na Iran Sun Bayyana Sabon Salon Mayar Da Martani Kan Isra’ila
  • Wakilin Sin A IAEA Ya Yi Tir Da Harin Isra’ila Kan Cibiyoyin Sarrafa Nukiliyar Iran
  • Muhimmanci, Tasiri Da Kuma Amfanin Jigida Ga Mata
  • Gwamnati Ta Yi Barazanar Matakai Masu Tsauri Kan Masu Fasa Bututun Mai
  • Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025
  • Gwamnatin Bauchi Ta Fara Shirin Kirkirar Sabbin Masarautu Da Sarakuna Da Gundumomi
  • Ƴansanda Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 2, Sun Ceto Mutane 11 A Delta Da Katsina
  • Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6