Pezeshkian: Iran za ta magance matsalolinta ne ta hanyar dogaro da kanta
Published: 14th, February 2025 GMT
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya yi gargadin cewa makiya kasarsa suna neman murkushe al’ummar kasar ta hanyar takunkumi da barazana.
Pezeshkian ya bayyana hakan ne a wata ganawa da ta yi da masana da masu fada aji na lardin Bushehr da ke kudancin kasar a ranar Alhamis , inda ya ce “Makiya suna son mu ulakanta a gabansu ta hanyar takunkumi da barazana, amma ba za mu yi kasa a gwiwa ba, kuma za mu magance matsalolinmu ta hanyar dogaro da jama’a.
Ya yi kakkausar suka kan irin matakan da Amurka ke dauka a kan Iran wadanda suke karo da juna, yana mai cewa shugaban Amurka Donald Trump na ikirarin cewa yana son tattaunawa da Iran amma a lokaci guda ya kakabawa Tehran takunkumi mafi tsauri.
“Ba ma son wani ya sanya mana takunkumi,” in ji Pezeshkian, ya kara da cewa, “Ba wai idan Amurka ta kakaba mana takunkumi ba, ba za mu iya yin komai ba. Za mu tafiyar da kasar ta hanyar dogaro da karfin cikin gida.”in ji Pezeshkian.
Ya nanata manufofin Iran na yin mu’amala da dukkan kasashe cikin lumana da ‘yan uwantaka, yana mai jaddada cewa, “Muna kokarin kulla kyakkyawar alaka da abokantaka da makwabta.”
Shugaban ya kara da cewa hadin kai, mu’amala da tsare-tsare na taka muhimmiyar rawa wajen magance matsalolin cikin gida.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Pezeshkiya: Iran A Shirye Take Don Mu’amala Amma Bazata Bar Hakkinta Ba
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkiyan ya bayyana cewa Iran a shirye take ta fadada hulda da kasashen turai, amma kuma wannan ba zai sa ta saryar da hakkinta na sarrafa makamashin nukliya karshen dokokin kasa da kasa wadanda suka amince mata ta yi haka ba.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto shugaban yana fadar haka a yau Litinin a lokacinda yake ganaw da sabon jakadan kasar Faransa a Tehran pierre Cochard wanda ya mika masa tarkardun fara aikinbsa.
Shugaban ya kara da cewa an takurawa kasar Iran dangane da shirinta na makamashin nukliya a bayan. Amma daga yanzun kuma ba zata amince da irin takurawa ta bay aba.
Ya kuma bayyana cewa tattaunawa tsakanin Iran da kasashe uku na turai wato Faransa da Jamus da kuma Burtaniya, saboda samun fahintar juna da kuma daukewa kasar takunkuman tattalin arzikinn da turawan suka dora mata.