’Yan Najeriya 52,000 za su sauke farali a 2025
Published: 13th, February 2025 GMT
Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON), ta tabbatar da cewa an tanadar wa maniyyatan Najeriya 52,000 guraben aikin Hajjin na shekarar 2025.
Wannan na cikin wata sanarwa da Mataimakiyar Daraktan Bayanai ta NAHCON, Fatima Sanda Usara, ta fitar.
An kama likita kan laifin yi wa ’yan bindiga magani a Katsina Kwastam ta lalata magungunan biliyan N100 a RibasTa ce hukumar ta riga ta biya kuɗin gurabe 26,287 na maniyyata, sannan ta tanadi wasu 26,000, da za a tabbatar da su gaba ɗaya kafin ranar 13 ga watan Fabrairu, 2025.
Domin cika wa’adin da Hukumar Aikin Hajji da Umrah ta Saudiyya ta bayar, Shugaban NAHCON, Farfesa Abdullahi Saleh Usman, ya tafi Makka domin ƙulla yarjejeniya.
Ya rattaba hannu kan yarjejeniyar a ranar 17 ga watan Janairu, 2025, bayan tuntuɓar shugabannin hukumar a jihohi da wakilin fadar shugaban ƙasa.
Shugaban ya tabbatar da ƙulla yarjejeniya da waɗanda za su kasance masu hidima tun da wuri don guje wa fuskantar tsaiko.
Wannan matakin yana da muhimmanci saboda ana sa ran fara aikin samar da biza ga maniyyata daga ranar 19 ga watan Fabrairu.
Shugaban NAHCON ya gode wa Mataimakin Shugaban Ƙasa, bisa goyon baya da taimakon da yake bai wa hukumar.
Ya ce hukumar za ta ɗauki matakan da suka dace don tabbatar da cewa maniyyata sun samu damar yin Hajji cikin sauki da kwanciyar hankali.
Ya kuma buƙaci su ci gaba da bibiyar kafofin sadarwa na NAHCON don samun sabbin bayanai.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Farfesa Pakistan Kasar Saudiyya tabbatar da
এছাড়াও পড়ুন:
Hajjin 2025: Yadda Alhazan Nijeriya 7 Suka Rasa Rayukansu A Saudi Arabiya
Duk da cewa, yanayin zafi ya yawaita a kasar ta Saudiyya, yayin gudanar da aikin Hajjin 2025, koda-yake; akasarin wadanda suka mutu daga Nijeriyar tsofaffi ne.
Rasuwar farko da aka sanar ta wani Alhaji ce daga Jihar Oyo, Alhaji Sulaimon Hamzat, wanda ya rasu a ranar 17 ga Mayun 2025 a kasar ta Saudiyya.
Na biye da shi kuma daga Jihar Abiya ne, mai suna Alhaji Saleh, Shugaban Kasuwar Shanu ta Lokpanta, wanda ya rasu a garin Makka a daren ranar Litinin 26 ga watan Mayun 2025.
Bayan haka kuma, sai wata Hajiya mai shekaru 75 daga Jattu Uzairue a Karamar Hukumar Etsako ta yamma da ke Jihar Edo, Adizatu Dazumi, wadda ta mutu a ranar Litinin 26 ga Mayun 2025, bayan gajeriyar rashin lafiya.
An samu rahoton cewa, Dazumi ta kamu da rashin lafiya jim kadan bayan kammala dawafi, inda aka garzaya ta ita zuwa asibitin Sarki Fahad da ke Makka a ranar Lahadi, washegari kuma ta mutu.
Haka zalika, wata Hajiya daga Jihar Filato ta rasu a birnin Makka da ke Saudiyya, yayin gudanar da wannan aiki Hajjin 2025.
Marigayiyar, mai suna Hajiya Jamila Muhammad, ta rasu ne sakamakon cutar Siga da ke fama da shi a asibitin Sarki Abdul’aziz da ke birnin Makka.
Kwana daya kafin fara aikin Hajjin 2025, wani Alhaji daga Jihar Kano mai suna Shu’aibu Jibrin, ya rasu a garin Makka.
Haka nan kuma, wani Alhajin Nijeriya ya rasu a filin Arfa.
A cewar Shugaban Hukumar Alhazai ta Nijeriya, Farfesa Abdullahi Saleh Usman, “Mun samu labari mara dadi cewa; mun rasa mahajjatanmu a yau Arfat, dayan kuma ya rasu kafin mu bar Makka,” in ji shi.
Ya kuma ce, mutuwar Alhazan daga Allah ne; inda ya kawar da rade-radin da ake yin a cewa, zafin rana ne ya haddasa su.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp