Gwamnatin Zamfara Na Biyan Ma’aikatan Bogi N193.6m Duk Wata
Published: 13th, February 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Zamfara ta bankaɗo ma’aikatan bogi 2,363 da ke karɓar jimillar N193,642,097.19 a kowane wata bayan gudanar da tantancewar ma’aikatan gwamnati.
Gwamna Dauda Lawal ya kafa kwamitin tantance ma’aikata a watan Agustan bara don tabbatar da biyan mafi ƙarancin albashi na N70,000. Kakakin gwamnan, Sulaiman Idris, ya bayyana cewa binciken ya nuna akwai ƙananan yara 220 da ke karɓar albashi a matsayin ma’aikatan gwamnati.
Rahoton kwamitin ya tabbatar da cewa an tantance ma’aikata 27,109, yayin da 2,363 suka kasance ma’aikatan bogi, 1,082 sun dace su yin ritaya, 395 na aikin kwantiragi, 261 ba su cikin jerin ma’aikata, 213 suna hutun karatu, 220 ƙanana ne, sannan 67 suna aiki a wasu wurare. Binciken ya kuma gano cewa ma’aikata 75 sun samu aiki ba bisa ƙa’ida ba, kuma dukkansu ƙanana ne a lokacin da aka ɗauke su aiki.
Kwamitin ya bada shawarar dakatar da ma’aikata 207 da ba a tantance ba, waɗanda ake biyansu N16,370,645.90 a kowane wata. Haka nan, an gano ma’aikata 12 a cikin jerin masu albashi amma ba su cikin bayanan ma’aikata, inda suke karɓar N726,594 a kowane wata. Gwamnati ta ce za ta ci gaba da wannan tantancewa don tabbatar da gaskiya da rikon amana, musamman duba da fara biyan mafi ƙarancin albashi daga watan Maris.
এছাড়াও পড়ুন:
Rashin tsaro: Gwamnan AbdulRahman Ya Gana Da Sarakuna Masu Daraja Ta Daya A Jihar Kwara
“Gwamnati ta amince da hada hannu da shugabannin al’umma na cikin gida domin tabbatar da tsaro.
“Muna gode muku kan abin da kuke yi. Amma muna bukatar Sarakuna su yi magana da mutanenmu kan kokarin da dukkanmu muke yi don kare al’ummominmu daga masu kutse.”
Gwamnan ya yi kira da a inganta hadin gwiwa a tsakanin al’umma da hukumomin tsaro domin kare rayuka da dukiyoyi.
Mataimakin Shugaban Majalisar Sarakunan Jihar Kwara, Alhaji Ibrahim Bologi II, wanda shi ne Etsu Patigi, ya yaba wa gwamnan bisa hada gwiwa da su domin tabbatar da tsaro a jihar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp