Babban Burinmu Shi Ne Tattara Naira Biliyan 100 A Bana – Dr. Zaid Abubakar
Published: 13th, February 2025 GMT
Hukumar tara haraji ta jihar Kano (KIRS) ta sanar da wani gagarumin shiri na kara yawan kudaden shiga na jihar zuwa sama da Naira biliyan 100 nan da shekarar 2025.
Shugaban hukumar Dr. Zaid Abubakar ne ya bayyana hakan a yayin da hukumar ke bitar ayyukan hukumar na shekarar 2024 da kuma tsare-tsarenta na shekarar 2025.
A cewar Abubakar, KIRS ta bullo da tsare-tsare na matsakaita da kuma na dogon lokaci domin bunkasa kudaden shiga na jihar.
Shirin tara kudaden shiga na matsakaicin zango na nufin tara sama da Naira biliyan 100 a shekarar 2025, inda ake sa ran za ta haura Naira biliyan 200 a shekaru masu zuwa.
Musamman ma, gwamnatin jihar tace tana son su hado hancin naira biliyan 75 a shekarar 2025, amma KIRS ta kuduri aniyar wuce wannan buri.
Ya ce don cimma wannan manufa, KIRS na da niyyar yin amfani da fasaha a matsayin wani bangare na kokarin da ta ke yi na aiki da dabarun zamani.
“Hukumar tana shirin amfani da fasahar zamani ta ICT don tsarin sarrafa bayanai da haɓaka tattara kudaden shiga da bin diddigi da ci gaba, da kuma tabbatar da ingantaccen gudanarwa.”
“Gwamnatin jihar Kano kuma tana shirin sake duba dokokin samar da kudaden shiga na jihar domin karfafa kudaden shiga.”
Abubakar ya lura cewa gwamnan ya amince da sake duba wadannan dokoki, wanda ake sa ran kammalawa kafin karshen watanni 3 na farko na shekarar 2025.
Abdullahi Jalaluddeen Kano/WABABE
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Haraji a shekarar 2025 Naira biliyan
এছাড়াও পড়ুন:
Babban Hafsan Soji Ya Ƙalubalanci Sabbin Sojoji Da Su Shirya Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda
“Yayin da kuka fita a yau kuma kuka samu matsayinku a wannan ma’aikata mai daraja, ku sani cewa za ku zama wani bangare na hanyoyin magance kalubalen ta’addanci da ‘yan tada kayar baya acikin al’ummarmu, don haka duk inda aka tura ku, tilas ne ku aiwatar da abinda aka horar da ku, kuma ku nuna jajircewa wajen fuskantar matsaloli.
“Tafiyar mil dubu tana farawa ne da taku daya, don haka, tafiyarku ta fara ne a ranar 13 ga watan Janairun 2025, lokacin da kuka fara amsar horo na aikin soji, an shirya muku duk wani abu da za ku iya fuskanta na kalubale, kuma ina mai tabbatar muku da cewa, za ku fuskanci kalubalen da da farko zaku ga kamar ba za a iya shawo kansu ba. Amma kuna jajircewa, sai su zama tarihi”. In ji shi
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp