Ƙungiyar malamai ta NUT-FCT da ma’aikatan ƙananan hukumomi na NULGE sun fara yajin aiki na dindin a yau Alhamis, sakamakon gazawar shugabannin ƙananan hukumomi wajen aiwatar da sabon albashi mafi ƙarancin na ₦70,000 da aka amince da shi tun Disamba 2024.

Ƙungiyoyin sun koka cewa duk da cewa sauran ma’aikatan FCT sun fara karɓar sabon albashin, an bar malaman firamare da ma’aikatan ƙananan hukumomi a baya.

Sun ce sun ba shugabannin isasshen lokaci domin su cika alƙawarin da suka ɗauka amma sun kasa, don haka suka yanke shawarar ci gaba da yajin aiki har sai an biya su hakkokinsu.

Yadda Jami’an Tsaro Suka Fara Gyara Wa ‘Yan Jari Bola Zama A Abuja… Hukumar FCTA Ta Rufe Asibitin Da Ke Aiki Ba Bisa Ka’ida Ba A Kuje

A sakamakon yajin aikin, an rufe makarantu a sassa daban-daban na FCT, inda malamai suka sallami ɗalibai. Wata malama, Mrs. Ene Igado, ta ce malaman firamare na L.E.A ana yi musu babbar wariya idan aka kwatanta da takwarorinsu na UBEB, duk da cewa su ne ke yin mafi yawan aiki.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Magidanci ya kuɓuta bayan wata 7 a hannun ’yan bindiga

’Yan bindiga sun sako wani magidanci da suka yi garkuwa da shi da amaryarsa na tsawon wata bakwai, bayan sun bindige matar tasa tare da karɓar kuɗin fansa Naira miliyan 30 daga iyalansa.

A watan Oktobar 2024 ne ’yan bindiga suka yi garkuwa da mutumin suna Yakubu Dada tare da amaryarsa, a yayin da ma’auratan ke tafiya a kan babban titin zuwa Kontagora a Jihar Neja.

A lokacin ’yan bindigar sun buƙaci kuɗin fansa Naira miliyan 10 daga iyalan mutumin, wanda tsohon ma’aikacin gwamnati ne.

Ba su sako shi ba sai a ranar Litinin, bayan da suka karɓi ƙarin Naira miliyan 20 daga iyalansa, jimilla Naira miliyan 30 ke nan.

A lokacin da suka yi garkuwa da ma’auratan sun buƙaci Naira miliyan 10, amma bayan iyalansa sun yi karo-karo sun biya, sai ’yan ta’addan suka nemi ƙarin Naira miliyan 20 da sababbin babura ƙirar Bajaj, sa’nnna suka yi barazanar kashe ma’auratan idan ba a ba su ba.

A farkon watan Mayu 2025, suka bindige amaryar tasa mai suna Lami, a ƙoƙarinsu na matsa wa iyalan su biya musu buƙata.

Uwar gidarsa mai suna Maimuna, ta tabbatar wa Aminiya cewa an sake shi a wani daji da ke kusa da yankin Kotonkoro a Ƙaramar Hukumar Mariga ta Jihar Neja, bayan da iyalan suka biya ƙarin Naira miliyan 20.

Malama Maimuna ta bayyana farin cikinsu, amma ta ce Malam Yakubu bai riga ya ya iso gida ba a lokacin.

Ta bayyana cewa a watan Nuwambar 2024 sai da suka sayar da kusan duk abin da suka mallaka domin haɗa Naira miliyan 10 da aka buƙata, wanda ƙanin mijin nasu ya kai wa ’yan bindigar a wani daji a Jihar Kebbi.

Ta ce bayan nan ne ’yan ta’ddan suka nemi ƙarin Naira miliyan 60 amma daga ƙarshe aka daidaita da su a kan Naira miliyan 20 da sababbin babura guda huɗu, buƙatar a iyalan suka yi ƙoƙarin biya kafin a sako shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 
  • Barazanar Yajin Aiki: Abuja da wasu jihohi 3 za su faɗa cikin duhu
  • Sojojin HKI Suna Ci Gaba Da Kashe Falasdinawa Wadanda Suke Jin Yunwa A Gaza
  • Babban Zauren MDD Ta Zabi Kasashen Congo Da Liberian Na Zama Mambobi A Kwamitin Tsaro
  • Tinubu ya gana da Fubara a Legas
  • DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja
  • ROOSC Ta Kaddamar Da Rabon Kayan Koyon Karatu A Kaduna
  • Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya
  • Ambaliyar Mokwa: Yawan mutanen da suka salwanta ya haura 700
  • Magidanci ya kuɓuta bayan wata 7 a hannun ’yan bindiga