Aminiya:
2025-05-24@16:51:10 GMT

Majalisa na neman rushe ƙudirin ƙara kuɗin kira da data

Published: 12th, February 2025 GMT

Majalisar Wakilai ta buƙaci Hukumar Kula da Sadarwa (NCC) ta janye ƙarin kashi 50 na kuɗin waya da data da ta amincewa kamfanonin sadarwa su yi.

Wannan dai na zuwa ne a yayin da ɗan majalisar daga Jihar Bayelsa, Oboku Oforji ya gabatar da ƙudirin kan lamarin.

Majalisar ta ce ƙarin bai kamata ba a wannan lokacin, saboda har yanzu babu tsayayyen layin waya mai sabis mai kyau a cikinsu.

Garkuwa da Mutane: An kama ɗan shekara 13 a wurin rajistar layin waya Netanyahu ya bai wa Hamas wa’adin sakin Isra’ilawan da take garkuwa da su

A don haka ne majalisar ta buƙaci NCC da Ministan Sadarwa, Bosun Tijani, su dakatar da ƙarin saboda matsin tattalin arzikin da ‘yan Najeriya ke fama da shi.

Alƙaluma dai na nuna daga watan Disambar 2023 zuwa yanzu, jimillar ‘yan Najeriya miliyan 224 ne ke amfani da layukan waya.

Alƙaluman sun kuma nuna MTN ne ka kan gaba da kashi 38.79 da adadin kwastamomi miliyan 87, sai Glo da Airtel masu miliyan 61, sai 9mobile mai miliyan 13.9.

Daga cikin kamfanonin kuma, MTN tuni ya fara ɗabbaka ƙarin kashi 50 akan kuɗin data da kiran waya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kamfanonin sadarwa Karin kudin data a Najeriya Majalisar Wakilai Sadarwa

এছাড়াও পড়ুন:

 MDD Ta Nuna Damuwa Akan Tabarbarewar Yanayin “Yan Hijira A Gabashin  Kasar Chadi

MDD ta bayyana cewa; Da akwai damuwa mai zurfi akan halin da ‘yan Hijirar Sudan suke ciki a gabashin kasar Chadi saboda rashin masu bayar da kudaden taimakon kula da su.

Ma’aikatan MDD a fagen ayyukan ceto sun ce ana samun kwararar ‘yan hijira daga Sudan zuwa gabashin kasar ta Chadi, da kuma ‘yan kasar ta Chadi da suke komawa gida.

Tun da yaki ya barke a Sudan zuwa yanzu an yi rijistar kwararar ‘yan Sudan masu yawa. A cikin wata daya kadai ‘yan Sudan  su dubu 55, sai kuma ‘yan asalin Chadi da su ka koma gida zuwa Jahar Inidy da yankin Fira, a gabashin kasar, da su kuma sun kai dubu 39.

Sanarwar ta MDD ta ci gaba da cewa; Wannan sabon adadin ya karu ne akan wasu ‘yan hijirar miliyan daya  da sun dade da shiga gabashin Chadi, tun daga fara yakin basasar Sudan a a tsakiyar watan Aprilu na 2023.

Mai Magana da yawun MDD Stephen Dujarric ya ce; siyasar da kasar Chadi take aiki da ita bude kofofinta ga ‘yan hijirar ne ya bayar da wannan damar.

Haka nan kuma ya bayyana cewa wuraren da aka ware domin tarbar ‘yan hijirar a gabashin Sudan din sun yi kadan’ sannan ya kara da cewa; mafi yawancin masu kwararowar mata ne da kananan yara da su ka kadu saboda yakin da ake yi a can Sudan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mace ta damfari masu neman aikin gwamnati Naira miliyan 250
  • Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • A Yemen An Yi Gangamin Miliyoyin Mutane Na Nuna Goyon Bayan Falasdinawa
  •  Ana Mayar Da Martani Akan Dan Majalisar Amurka  Da Ya Yi Kira A Jefa Bom Din Nukiliya A Gaza
  • Kotu ta bai wa EFCC izinin binciken sayar da filin musabaƙar Alƙur’ani na N3.5bn a Kano
  • Yan Majalisar Tarayya Na Katsina Sun Mara Wa Gwamna Dikko Radda Baya Don Takarar Zango Na Biyu
  • An kama jami’in Hukumar NRC da laifin satar waya
  •  MDD Ta Nuna Damuwa Akan Tabarbarewar Yanayin “Yan Hijira A Gabashin  Kasar Chadi
  • Mai kwashe sharar da ya shekara 40 yana tara kuɗin Hajji ya isa Saudiyya tare da matarsa
  • Yadda ‘Yan Majalisa Ke Cusa Ayyuka Marasa Amfani A Kasafin Kuɗi – Rahoto