Majalisa na neman rushe ƙudirin ƙara kuɗin kira da data
Published: 12th, February 2025 GMT
Majalisar Wakilai ta buƙaci Hukumar Kula da Sadarwa (NCC) ta janye ƙarin kashi 50 na kuɗin waya da data da ta amincewa kamfanonin sadarwa su yi.
Wannan dai na zuwa ne a yayin da ɗan majalisar daga Jihar Bayelsa, Oboku Oforji ya gabatar da ƙudirin kan lamarin.
Majalisar ta ce ƙarin bai kamata ba a wannan lokacin, saboda har yanzu babu tsayayyen layin waya mai sabis mai kyau a cikinsu.
A don haka ne majalisar ta buƙaci NCC da Ministan Sadarwa, Bosun Tijani, su dakatar da ƙarin saboda matsin tattalin arzikin da ‘yan Najeriya ke fama da shi.
Alƙaluma dai na nuna daga watan Disambar 2023 zuwa yanzu, jimillar ‘yan Najeriya miliyan 224 ne ke amfani da layukan waya.
Alƙaluman sun kuma nuna MTN ne ka kan gaba da kashi 38.79 da adadin kwastamomi miliyan 87, sai Glo da Airtel masu miliyan 61, sai 9mobile mai miliyan 13.9.
Daga cikin kamfanonin kuma, MTN tuni ya fara ɗabbaka ƙarin kashi 50 akan kuɗin data da kiran waya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Kamfanonin sadarwa Karin kudin data a Najeriya Majalisar Wakilai Sadarwa
এছাড়াও পড়ুন:
NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a Legas
Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Najeriya (NDLEA) ta kama wani ɗan ƙasar Indiya tare da wasu mutane uku bisa zargin shigo da ƙwayoyin Tramadol da aka ƙiyasta darajarsu ta kai naira biliyan uku (N3bn) zuwa cikin ƙasar.
A cewar NDLEA, wannan shi ne kamen ƙwayoyi mafi girma da hukumar ta yi a cikin shekarar nan, lamarin da ke nuna yadda safarar miyagun ƙwayoyi ke ƙaruwa a ƙasar.
Peter Obi ya kai wa Obasanjo ziyara An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a NijarCikin wata sanarwa da hukumar ta fitar, ta bayyana cewa jami’anta sun kama mutanen ne a filin jirgin sama na Murtala Muhammad da ke Legas, bayan sun samu bayanan sirri da suka taimaka wajen gano su.
NDLEA ta bayyana cewa ƙwayoyin Tramadol ɗin da aka gano an shigo da su ne cikin kwalaye a matsayin maganin multivitamins, yayin da ake ƙoƙarin fitar da su daga filin jirgin a wasu manyan motoci.
“Ƙwayoyin da aka kama ba su da wata alaƙa da amfani na lafiya, waɗanda aka shigo da su a ɓoye a matsayin maganin rage kasala da ƙara kuzari (multivitamins),” in ji sanarwar NDLEA.
Rahotanni sun nuna cewa a da likitoci na bayar da Tramadol ne don rage zafi da raɗaɗin ciwo, amma yanzu ta zamo annoba musamman a tsakanin matasa, wadda ke haddasa mummunan maye da illa ga lafiya.
Hukumar ta nuna damuwa game da yadda yawan masu amfani da Tramadol ke ƙaruwa ba wai a Najeriya kaɗai ba, har ma a wasu ƙasashen Afirka, duk da illolin da ƙwayar ke haddasawa, kamar matsalolin taɓin hankali ko ma rasa rai gaba ɗaya.