Garkuwa da Mutane: An kama ɗan shekara 13 a wurin rajistar layin waya
Published: 12th, February 2025 GMT
An cafke wani saurayi mai kimanin shekaru 13 bayan ya je rajistar layin wayar salula a yankin ’Yan Katako da ke Ƙaramar Hukumar Jos ta Arewa.
Rundunar ’yan sandan Filato ce ta yi wa manema labarai holen saurayin mai suna Umar Hashim tare da wasu mutum shida da ake zargi da garkuwa da kuma kisan wani mai suna Tasiu Abdullahi a ranar 20 ga watan Disamba.
Sai dai da yake yi wa manema labarai jawabi, Hashim ya bayyana cewa jami’an tsaron har gida suka je suka kama shi da cewa an yi amfani da lambar wayarsa wajen karɓar kuɗin fansar mutumin da aka kashe, wato Tasiu Abdullahi.
Hashim ya bayyana cewa tun a ranar 12 ga watan Disamba ya je sayen sabon layin wayar a wurin wani mai suna Usman Abdullahi kuma ya nemi a yi masa rajistarsa.
Sai dai mai rajistar layin ya nemi ya dawo wani lokacin saboda rashin sabis tare da neman ya taho da shaidar ɗan ƙasa ta NIN ta wani ɗan uwansa la’akari da ƙarancin shekarunsa.
“Hashim ya ce, “na dawo na ɗauki shaidar NIN ɗin yayana na koma wurin rajistar layin.
“Sai dai mai rajistar layin ya shaida min ana kan aikin nawa sannan ya aike ni sayen katin waya.
“Bayan na dawo ya [mai rajistar] ce min an kammala aiki kuma ya ba ni layin da aka yi min rajistar na kama gaba na.
“Ba ni da wata masaniyar cewa an yi amfani da layin nawa wajen neman kuɗin fansa kamar yadda jami’an tsaron suke iƙirari.”
A nasa jawabin, mai rajistar layin, Usman Abdullahi, ya ce yaron ya sayi sabon layin ne a wurinsa amma ya bai wa wasu abokansa layin an kammala rajistar.
Sai dai Abdullahi ya ce ba shi da masaniyar abin da abokan suka da layin da suka karɓa kafin dawo wa yaron kayansa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: garkuwa da mutane Jihar Filato Rajistar Layi rajistar layin mai rajistar
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga sun kashe mutum 5 a sabon hari a Alkaleri
Mahara sun kashe akalla mutane biyar a Dajin Madam da ke yankin Karamar Hukumar Alkaleri ta Jihar Bauchi.
Wannan na zuwa ne bayan a makon jiya ’yan bindiga sun kutsa kauyukan da ke kusa da garin Mansur a karamar hukumar, inda suka kashe mutane hudu, suka kwashe kayayyaki a shagunansu.
Daga bisani ’yan sanda sun sun bi su, inda suka fatattake su suka gudu zuwa cikin kungurmin Dajin Madam.
Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Abdulkadir Mohammed ne ya sanar da mutuwar mutanen a yayin taron zaman lafiya da aka gudanar a garin Nahutan Darazo a kokarinsa na sasanta rikicin baya-bayan nan tsakanin manoma da makiyaya da ya yi sanadin jikkatar wassu mutane a Darazo.
Gwamnan ya kuma nuna matuqar damuwarsa kan bisa yadda mafarauta da a baya suke goyon bayan ayyukan tsaro na kare dazuzzukan jihar a yanzu haka suka shiga cikin rikici da manoma.
Wani mutum ya mutu yayin raba faɗar ma’aurata ’Yan sa-kai aƙalla 100 da ’yan sanda 30 sun mutu a bakin aiki a Katsina —GwamnatiGwamna ya ce gwamnatinsa tare da hadin gwiwar hukumomin tsaro da kungiyoyin ’yan banga sun dukufa wajen kwato dabbobin da aka sace da kuma wanzar da zaman lafiya a yankunan karkara.
Ya yaba wa mafarautan yankin bisa ci gaba da goyon bayan da suke bayarwa wajen tabbatar da kare dazuzzukan. “Kun taimaka mana wajen kare dazuzzukanmu a Toro, Ningi, Duguri, Yankari, Kirfi, ba a Darazo kadai ba.
“A ranar Litinin ne ’yan bindiga suka kashe mutane biyar a Dajin Madam, wanda ke kan iyaka da Taraba, Filato, da Bauchi-Alkaleri.
“Me ya sa ba ku taimaka mana a can ba? Muna fuskantar kalubale sosai a dazuzzukanmu. Bauchi tana da dazuzzukan sama da hekta miliyan hudu da tsaunukan da ba kowa zai iya shiga ba, sai ku.”
Gwamna Bala ya alaqanta wannan tashin hankali da kwararowar jama’a daga wasu jihohi zuwa Bauchi, tare da qaruwar yawan jama’a, lamarin da ya qara matsin lamba ga kasa da albarkatun kasa.
Yace Yan bindigan yanzu Suna cikin Jihar Taraba ne,kuma Gwamnan Taraba munyi Magana dashi zamu Yi hadin guiwar Domin a fatattakesu a wurin”
Kan rikicin manoma da makiyaya a Darazo da Sade kuma, gwamna yya kaddamar da wani babban kwamiti da zai binciki rikicin na dajin Aliya, Yautare, da Farin Ruwa na Karamar Hukumar Darazo.
Mataimakin gwamnan jihar, Muhammad Auwal Jatau, wanda kuma shi ne shugaban kwamitin ne ya kaddamar da kwamitin a gidan gwamnati da ke Bauchi, inda ya kuma bukaci ’yan kwamitin da su gudanar da ayyukansu cikin himma, adalci, da rashin son kai.