Garkuwa da Mutane: An kama ɗan shekara 13 a wurin rajistar layin waya
Published: 12th, February 2025 GMT
An cafke wani saurayi mai kimanin shekaru 13 bayan ya je rajistar layin wayar salula a yankin ’Yan Katako da ke Ƙaramar Hukumar Jos ta Arewa.
Rundunar ’yan sandan Filato ce ta yi wa manema labarai holen saurayin mai suna Umar Hashim tare da wasu mutum shida da ake zargi da garkuwa da kuma kisan wani mai suna Tasiu Abdullahi a ranar 20 ga watan Disamba.
Sai dai da yake yi wa manema labarai jawabi, Hashim ya bayyana cewa jami’an tsaron har gida suka je suka kama shi da cewa an yi amfani da lambar wayarsa wajen karɓar kuɗin fansar mutumin da aka kashe, wato Tasiu Abdullahi.
Hashim ya bayyana cewa tun a ranar 12 ga watan Disamba ya je sayen sabon layin wayar a wurin wani mai suna Usman Abdullahi kuma ya nemi a yi masa rajistarsa.
Sai dai mai rajistar layin ya nemi ya dawo wani lokacin saboda rashin sabis tare da neman ya taho da shaidar ɗan ƙasa ta NIN ta wani ɗan uwansa la’akari da ƙarancin shekarunsa.
“Hashim ya ce, “na dawo na ɗauki shaidar NIN ɗin yayana na koma wurin rajistar layin.
“Sai dai mai rajistar layin ya shaida min ana kan aikin nawa sannan ya aike ni sayen katin waya.
“Bayan na dawo ya [mai rajistar] ce min an kammala aiki kuma ya ba ni layin da aka yi min rajistar na kama gaba na.
“Ba ni da wata masaniyar cewa an yi amfani da layin nawa wajen neman kuɗin fansa kamar yadda jami’an tsaron suke iƙirari.”
A nasa jawabin, mai rajistar layin, Usman Abdullahi, ya ce yaron ya sayi sabon layin ne a wurinsa amma ya bai wa wasu abokansa layin an kammala rajistar.
Sai dai Abdullahi ya ce ba shi da masaniyar abin da abokan suka da layin da suka karɓa kafin dawo wa yaron kayansa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: garkuwa da mutane Jihar Filato Rajistar Layi rajistar layin mai rajistar
এছাড়াও পড়ুন:
Sudan : Kasashen duniya na Allah wadai da cin zarafi a lokacin kama El-Fasher
Kwamitin Tsaro na Majalisar Dinkin Duniya ya yi Allah wadai da harin da aka kai wa garin El-Fasher da ke Darfur a ranar Alhamis, da kuma mummunan tasirin da ya yi ga fararen hula.
A cikin sanarwar da ya fitar, kwamitin ya nuna matukar damuwarsa game da karuwar tashin hankalin da ke faruwa a El-Fasher da kewaye, wanda Rundunar Taimakon Gaggawa (RSF) ta kwace iko da shi kwanan nan, kuma ya yi Allah wadai da ta’addancin da ake zargin dakarun RSF sun yi wa fararen hula, ciki har da kisan gilla da tsare mutane ba bisa ka’ida ba.
Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta ce ta “firgita da rahotannin kisan sama da marasa lafiya 460 da abokan aikinsu a asibitin haihuwa na El-Fasher a Sudan.”
A cikin wani bidiyo da aka fitar a ranar Laraba a shafukan sada zumunta, Janar Hemedti ya amince cewa sojojinsa sun aikata cin zarafi.
Da yake magana daga wani wuri da ba a bayyana ba, janar din, sanye da kayan soja, cewa “Na lura da keta haddi a El-Fasher,” inda ya sanar da kafa kwamitin bincike nan take.
Ya yi alƙawarin cewa za a kama duk wani soja da aka samu da laifin cin zarafi kuma a gurfanar da shi a gaban kotu.
Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya António Guterres ya bukaci bangarorin da su hanzarta shiga tattaunawa a cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta.
kungiyar likitocin Sudan, ta ce “Adadin wadanda suka mutu ya wuce 2,000 a cikin kwanaki biyu na farko bayan da RSF ta shiga El-Fasher.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Ta Jaddada Bin Hanyar Diflomasiya Ko Da A Lokacin Yaki Ne Amma Ba Zata Amince Da Bin Umarni Ba October 30, 2025 Qalibaf: Amurka Tana Yaudarar Duniya Da Zaman Lafiya, Alhalin Tana Ci Gaba Da Kai Harin Wuce Gona Da Iri October 30, 2025 Ci Gaba Da Killace Gaza Bayan Tsagaita Bude Wuta Ya Janyo Mutuwar Mutane 1000 A Yankin October 30, 2025 Kungiyar Rapid Support Forces Ta Sanar Da Kafa Kwamitin Bincike Kan Cin Zarafin Al’umma A El Fasher October 30, 2025 An Kafa Dokar Ta Baci A Darul-Salam Saboda Tarzoman Zaben Shugaban Kasa A Tanzania October 30, 2025 Rasha Da Amurka Sun Sake Dawo Da Gwaje-gwajen Makaman Nukiliya October 30, 2025 Kasar Czech Ta Hana Wa Wani Sojan HKI Shiga Kasar Bisa Gargadin Faransa October 30, 2025 Sojojin HKI Sun Kutsa Kudancin Lebanon October 30, 2025 Adadin Falasdinawan Da Su Ka Yi Shahada A Cikin Sa’o’i 24 Sun Haura 100 October 30, 2025 Amurka Ta Hana Marubuci Dan Nigeria Wole Soyinka Izinin Shiga Amurka October 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci