Garkuwa da Mutane: An kama ɗan shekara 13 a wurin rajistar layin waya
Published: 12th, February 2025 GMT
An cafke wani saurayi mai kimanin shekaru 13 bayan ya je rajistar layin wayar salula a yankin ’Yan Katako da ke Ƙaramar Hukumar Jos ta Arewa.
Rundunar ’yan sandan Filato ce ta yi wa manema labarai holen saurayin mai suna Umar Hashim tare da wasu mutum shida da ake zargi da garkuwa da kuma kisan wani mai suna Tasiu Abdullahi a ranar 20 ga watan Disamba.
Sai dai da yake yi wa manema labarai jawabi, Hashim ya bayyana cewa jami’an tsaron har gida suka je suka kama shi da cewa an yi amfani da lambar wayarsa wajen karɓar kuɗin fansar mutumin da aka kashe, wato Tasiu Abdullahi.
Hashim ya bayyana cewa tun a ranar 12 ga watan Disamba ya je sayen sabon layin wayar a wurin wani mai suna Usman Abdullahi kuma ya nemi a yi masa rajistarsa.
Sai dai mai rajistar layin ya nemi ya dawo wani lokacin saboda rashin sabis tare da neman ya taho da shaidar ɗan ƙasa ta NIN ta wani ɗan uwansa la’akari da ƙarancin shekarunsa.
“Hashim ya ce, “na dawo na ɗauki shaidar NIN ɗin yayana na koma wurin rajistar layin.
“Sai dai mai rajistar layin ya shaida min ana kan aikin nawa sannan ya aike ni sayen katin waya.
“Bayan na dawo ya [mai rajistar] ce min an kammala aiki kuma ya ba ni layin da aka yi min rajistar na kama gaba na.
“Ba ni da wata masaniyar cewa an yi amfani da layin nawa wajen neman kuɗin fansa kamar yadda jami’an tsaron suke iƙirari.”
A nasa jawabin, mai rajistar layin, Usman Abdullahi, ya ce yaron ya sayi sabon layin ne a wurinsa amma ya bai wa wasu abokansa layin an kammala rajistar.
Sai dai Abdullahi ya ce ba shi da masaniyar abin da abokan suka da layin da suka karɓa kafin dawo wa yaron kayansa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: garkuwa da mutane Jihar Filato Rajistar Layi rajistar layin mai rajistar
এছাড়াও পড়ুন:
An kama ’yar Najeriya da laifin safarar ɗalibai 15 a Australia
Rundunar ’yan sandan ƙasar Australia ta kama wata ’yar asalin Najeriya da ke ƙasar Australia, Binta Abubakar bisa zarginta da safarar ɗalibai daga ƙasar Papua New Guinea tare da tilasta musu yin aikin da ba a biya a gonaki a faɗin jihar Ƙueensland da sunan bayar da tallafin karatu.
Binta mai shekara 56, an kama ta ne a ranar Laraba a filin jirgin saman Brisbane a lokacin da ta isa ƙasar Papua New Guinea, inda take zaune.
Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawar mutum bayan kwanaki 8 Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — FayemiKamen nata ya biyo bayan wani bincike na tsawon shekaru biyu da ƙungiyar masu fataucin bil-Adama ta AFP ta yankin Arewa, wacce ta ƙaddamar da bincike kan ayyukanta a watan Yulin 2022 bayan samun bayanai daga ’yan sandan Ƙueensland.
A cewar AFP, “Wani gungun ‘yan asalin Papua New Guinea (PNG) da suka yi ƙaura zuwa Australia don yin karatu, an yi zargin cewa an tilasta musu yin aiki ba tare da son ransu ba a gonaki.”
An ba da rahoton cewa matar mai izinin zama ƙasashen biyu ta yaudari aƙalla ƴan ƙasar PNG 15, masu shekaru tsakanin 19 zuwa 35, zuwa Australia tsakanin Maris 2021 da Yuli 2023 ta hanyar kamfaninta, BIN Educational Serɓices and Consulting, da kuma ta hanyar ba da guraben karatu na bogi.
Rahoton ya bayyana cewa, shafin intanet na kamfaninta ya yi iƙirarin bayar da “daidaitaccen tsarin zamani don ilimi, horarwa da kuma aikin yi.”
Sai dai ’yan sandan sun ce gaskiyar lamarin ya sha bamban sosai.
Da zarar sun isa Australia, an yi zargin cewa an tilasta wa ɗaliban su sanya hannu kan jerin takaddun doka da ke tilasta su su biya kuɗin da ke da alaƙa da karatun, kuɗin jirgi, aikace-aikacen samar da biza, inshora da kuma kuɗaɗen doka.”