Aminiya:
2025-05-01@04:24:46 GMT

An yi wa kashi 25 na matan Nijeriya kaciya

Published: 12th, February 2025 GMT

Masu fafutikar kare haƙƙin bil Adama da ƙwararru a fannin kiwon lafiya haɗi da fasihai a ɓangaren shari’a sun buƙaci a tsananta hukunci kan masu yi wa mata kaciya a Nijeriya.

Masu ruwa da tsakin sun yi kira da a ƙara wayar da kan al’umma domin ganin an daƙile kaciyar mata gaba ɗaya a ƙasar nan.

Garkuwa da Mutane: An kama ɗan shekara 13 a wurin rajistar layin waya DAGA LARABA: Dalilan Da Al’adar Zanen Fuska Ke Neman Gushewa A Kasar Hausa

A yayin wani taro da aka gudanar kan kawo ƙarshen kaciyar mata a Nijeriya, Nora Agbakhamen, wanda ta assasa Pulse Narrative, ta ce fiye da mata miliyan 200 a faɗin duniya sun fuskanci wani nau’i na kaciya, lamarin da ya shafi kashi 25 cikin 100 na matan Nijeriya.

Agbakhamen ta ce duk da cewa dokokin ƙasa da ƙasa sun ayyyana kaciyar mata a matsayin wani nau’i na cin zarafi da keta haddi, har yanzu matsalar na ci gaba da ta’azzara a sakamakon rashin tsananta hukunci.

A cewarta, akwai buƙatar a haɗa kai da duk masu ruwa da tsaki musamman tare da ƙwararru a fannin kiwon domin wayar da kan al’umma wajen ganin an kawo ƙarshen wannan matsalar.

Mohammed Abubakar na Masarautar Chokalin Fika da ke Jihar Yobe, ya ce sarakunan gargajiya tare da haɗin gwiwar ƙungiyoyi masu zaman kansu na ci gaba da wayar da kan al’ummominsu kan illolin da ke tattare da kaciyar mata.

Ya bayyana cewa Gwamnatin Yobe ta shimfiɗa dokoki masu tsanani kan masu yi wa mata kaciya domin ganin an shawo kan matsalar.

Yayin da yake bayyana rawar da sarakunan gargajiya suke takawa, ya buƙaci ƙarin haɗin gwiwa domin tunkarar wannan annoba ta hanyar wayar da kan al’umma da shimfiɗa dokoki masu tsanani.

Wata ma’aikaciyar jinya kuma mai fafutikar yaƙi da cin zarafin mata, Amina Waziri Abdullahi, ta bayyana kaciyar mata a matsayin wani nau’i na cin zarafi da yake da mummunan tasiri ga rayuwar mace.

Shi ma wani wani lauya kuma mai fafutikar kare haƙƙin mata, Kowoabi Takoni, ya buƙaci a sanya haddin da ya zarce Naira dubu 200 da a yanzu ake karɓa a wurin waɗanda aka kama da laifin.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: cin zarafi Kaciyar Mata kaciyar mata

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jadadda Cewa: Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kan Iran Zai Fuskanci Mayar Da Martani

Ministan harkokin wajen Iran ya jaddada cewa: Duk wani harin wuce gona da iri kan Iran zai fuskanci mayar da martani daidai da shi cikin gaggawa

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya tabbatar da cewa Iran na da kwarin gwiwa kan iya dakile duk wani yunkuri da wasu bangarorin ke yi na kawo cikas ga manufofinta na ketare.

Ministan harkokin wajen kasar Abbas Araqchi ya bayyana a cikin wata sanarwa cewa: Rudun gwamnatin yahudawan sahayoniyya, wadda take ganin za ta iya gindaya wa Iran abin da ya kamata ko kuma bai kamata ba, rudun tunani ne da ya yi nesa da hakikanin gaskiya, ta yadda bai cancanci mayar da martani ba.

Araqchi ya kara da cewa: “Duk da haka, jajircewar Netanyahu wani abin lura ne, a yayin da yake kokarin neman bayyana wa Shugaba Trump abin da zai iya ko kuma ba zai iya yi a diflomasiyyarsa da Iran ba!”

Ministan harkokin wajen ya yi nuni da cewa: “Abokanan Netanyahu a cikin tawagar Biden da ta gaza – wadanda suka kitsa makarkashiyar hana cimma yarjejeniya da Iran – suna kokarin nuna zaman tattaunawar da ake yi ba na kai tsaye ba da gwamnatin Trump a matsayin wani kuskure ne kuma tamkar hoton sauran yarjejeniyar nukiliya ce da aka gudanar.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Xi Ya Jaddada Muhimmancin Tsara Nagartaccen Shirin Raya Tattalin Arziki Da Zamantakewar Al’umma Tsakanin 2026-2030
  • Da Alamu Amurka Ta Fara Dandana Kudarta
  • Cinikayyar Hidima Ta Kasar Sin Ta Matukar Bunkasa A Rubu’in Farko Na Nana
  • Rashin tsaro: Gwamnan AbdulRahman Ya Gana Da Sarakuna Masu Daraja Ta Daya A Jihar Kwara 
  • Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno
  • Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Binciken Yawaitar Haɗurran Tankokin Man Fetur A Nijeriya 
  • Nijeriya Na Ke Yi Wa Biyayya Ba Wani Ko Jam’iyya Ba – El-Rufai
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jadadda Cewa: Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kan Iran Zai Fuskanci Mayar Da Martani
  • Akwai Ƙarin Gishiri A Yawan  Masu Sauyin Jam’iyya Zuwa APC – El-Rufai
  • Yadda matar gwamna ta sa mata gasar haihuwar ’yan uku