An yi wa kashi 25 na matan Nijeriya kaciya
Published: 12th, February 2025 GMT
Masu fafutikar kare haƙƙin bil Adama da ƙwararru a fannin kiwon lafiya haɗi da fasihai a ɓangaren shari’a sun buƙaci a tsananta hukunci kan masu yi wa mata kaciya a Nijeriya.
Masu ruwa da tsakin sun yi kira da a ƙara wayar da kan al’umma domin ganin an daƙile kaciyar mata gaba ɗaya a ƙasar nan.
Garkuwa da Mutane: An kama ɗan shekara 13 a wurin rajistar layin waya DAGA LARABA: Dalilan Da Al’adar Zanen Fuska Ke Neman Gushewa A Kasar HausaA yayin wani taro da aka gudanar kan kawo ƙarshen kaciyar mata a Nijeriya, Nora Agbakhamen, wanda ta assasa Pulse Narrative, ta ce fiye da mata miliyan 200 a faɗin duniya sun fuskanci wani nau’i na kaciya, lamarin da ya shafi kashi 25 cikin 100 na matan Nijeriya.
Agbakhamen ta ce duk da cewa dokokin ƙasa da ƙasa sun ayyyana kaciyar mata a matsayin wani nau’i na cin zarafi da keta haddi, har yanzu matsalar na ci gaba da ta’azzara a sakamakon rashin tsananta hukunci.
A cewarta, akwai buƙatar a haɗa kai da duk masu ruwa da tsaki musamman tare da ƙwararru a fannin kiwon domin wayar da kan al’umma wajen ganin an kawo ƙarshen wannan matsalar.
Mohammed Abubakar na Masarautar Chokalin Fika da ke Jihar Yobe, ya ce sarakunan gargajiya tare da haɗin gwiwar ƙungiyoyi masu zaman kansu na ci gaba da wayar da kan al’ummominsu kan illolin da ke tattare da kaciyar mata.
Ya bayyana cewa Gwamnatin Yobe ta shimfiɗa dokoki masu tsanani kan masu yi wa mata kaciya domin ganin an shawo kan matsalar.
Yayin da yake bayyana rawar da sarakunan gargajiya suke takawa, ya buƙaci ƙarin haɗin gwiwa domin tunkarar wannan annoba ta hanyar wayar da kan al’umma da shimfiɗa dokoki masu tsanani.
Wata ma’aikaciyar jinya kuma mai fafutikar yaƙi da cin zarafin mata, Amina Waziri Abdullahi, ta bayyana kaciyar mata a matsayin wani nau’i na cin zarafi da yake da mummunan tasiri ga rayuwar mace.
Shi ma wani wani lauya kuma mai fafutikar kare haƙƙin mata, Kowoabi Takoni, ya buƙaci a sanya haddin da ya zarce Naira dubu 200 da a yanzu ake karɓa a wurin waɗanda aka kama da laifin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: cin zarafi Kaciyar Mata kaciyar mata
এছাড়াও পড়ুন:
Majalisa ta ba NNPCL mako uku ya yi mata bayanin inda tirilyan 210 ta shiga
Kwamitin Majalisar Dattawa na bin Diddigi ya ba Kamfanin Mai na Kasa (NNPCL) wa’adin mako uku ya amsa tambayoyi kan rashin ba da ba’asi kan Naira tiriliyan 210 da ba a san inda suka shiga ba daga shekarar 2017 zuwa 2023.
An dai bayar da wa’adin ne ga shugaban kamfanin na kasa, Bayo Ojulari, wanda ya bayyana a gaban kwamitin ranar Talata, bayan ya bayar da hakuri kan rashin bayyanarsa yayin gayyatar da kwamitin ya yi masa a baya.
Yadda ’yan bindiga sun tarwatsa ƙauyuka sama da 10 a Katsina Gwamnatin Tinubu ta mayar da Arewa saniyar ware – ACFKwamitin, wanda ke karkashin jagorancin Ahmed Wadada Aliyu (Nasarawa), ya tsaya kai da fata cewa dole kamfanin ya bayyana inda kudaden suka shiga.
Ojulari dai ya ba kwamitin hakuri, inda ya ce yana bukatar karin lokaci kafin ya iya amsa tuhumar da aka yi masa har guda 19.
Ya kuma ce, “Da kadan na haura kwana 100 a matsayin shugaban wannan kamfanin. Ina bukatar karin lokaci kafin na iya zakulo bayanan da kuka bukata. Wannan kuma na zuwa ne a daidai lokacin da sauran tarin ayyuka ke jira na.
“Ni kaina ina bukatar fahimtar abubuwan da kaina kafin na iya bayar da amsa a kansu. Amma zan je na zauna da sauran ma’aikatana da suka dace mu tattauna domin bayar da abin da ake bukata,” in ji shugaban na NNPCL.
Kodayake mako hudu ya bukata, amma kwamitin ya ba shi mako uku ne domin ya gabatar da bayanan.
Da yake karin haske a kan kudaden, Sanata Wadada ya ce kudaden da ake magana a kan su rubi biyu ne, akwai Naira tiriliyan 103 da kuma Naira tiriliyan 107 da suke bukatar bayanan a kan su.
“Amma fa ba mu ce wadannan kudaden da ake magana a kan su sace su aka yi ko kuma sun bace ba. Abin da kwamitinmu kawai yake kokarin yi shi ne bincike domin gano yadda aka yi tusarrufi da su,” in ji Sanata Wadada.