Aminiya:
2025-11-03@04:07:45 GMT

An yi wa kashi 25 na matan Nijeriya kaciya

Published: 12th, February 2025 GMT

Masu fafutikar kare haƙƙin bil Adama da ƙwararru a fannin kiwon lafiya haɗi da fasihai a ɓangaren shari’a sun buƙaci a tsananta hukunci kan masu yi wa mata kaciya a Nijeriya.

Masu ruwa da tsakin sun yi kira da a ƙara wayar da kan al’umma domin ganin an daƙile kaciyar mata gaba ɗaya a ƙasar nan.

Garkuwa da Mutane: An kama ɗan shekara 13 a wurin rajistar layin waya DAGA LARABA: Dalilan Da Al’adar Zanen Fuska Ke Neman Gushewa A Kasar Hausa

A yayin wani taro da aka gudanar kan kawo ƙarshen kaciyar mata a Nijeriya, Nora Agbakhamen, wanda ta assasa Pulse Narrative, ta ce fiye da mata miliyan 200 a faɗin duniya sun fuskanci wani nau’i na kaciya, lamarin da ya shafi kashi 25 cikin 100 na matan Nijeriya.

Agbakhamen ta ce duk da cewa dokokin ƙasa da ƙasa sun ayyyana kaciyar mata a matsayin wani nau’i na cin zarafi da keta haddi, har yanzu matsalar na ci gaba da ta’azzara a sakamakon rashin tsananta hukunci.

A cewarta, akwai buƙatar a haɗa kai da duk masu ruwa da tsaki musamman tare da ƙwararru a fannin kiwon domin wayar da kan al’umma wajen ganin an kawo ƙarshen wannan matsalar.

Mohammed Abubakar na Masarautar Chokalin Fika da ke Jihar Yobe, ya ce sarakunan gargajiya tare da haɗin gwiwar ƙungiyoyi masu zaman kansu na ci gaba da wayar da kan al’ummominsu kan illolin da ke tattare da kaciyar mata.

Ya bayyana cewa Gwamnatin Yobe ta shimfiɗa dokoki masu tsanani kan masu yi wa mata kaciya domin ganin an shawo kan matsalar.

Yayin da yake bayyana rawar da sarakunan gargajiya suke takawa, ya buƙaci ƙarin haɗin gwiwa domin tunkarar wannan annoba ta hanyar wayar da kan al’umma da shimfiɗa dokoki masu tsanani.

Wata ma’aikaciyar jinya kuma mai fafutikar yaƙi da cin zarafin mata, Amina Waziri Abdullahi, ta bayyana kaciyar mata a matsayin wani nau’i na cin zarafi da yake da mummunan tasiri ga rayuwar mace.

Shi ma wani wani lauya kuma mai fafutikar kare haƙƙin mata, Kowoabi Takoni, ya buƙaci a sanya haddin da ya zarce Naira dubu 200 da a yanzu ake karɓa a wurin waɗanda aka kama da laifin.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: cin zarafi Kaciyar Mata kaciyar mata

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Tarayya Da Stellar Steel, Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Habaka Karafan Cikin Gida

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa October 31, 2025 Manyan Labarai Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar October 31, 2025 Manyan Labarai NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba
  • Kisan Kiristoci: Ba zan yaƙi ƙasar iyayena kan labaran ƙarya ba — Sojan Amurka
  • A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?
  • ‘An Kashe Masu Zanga-zanga Akalla 500 a Tanzania’
  • Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
  • Gwamnatin Tarayya Da Stellar Steel, Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Habaka Karafan Cikin Gida
  • Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa
  • Yan Nijeriya Na Ɗanɗana Kuɗarsu Kan Jinkirta Cire Tallafin Mai – Sarki Sanusi
  • An sake kama shi a cikin ’yan fashi kwana 5 da fitowa daga kurkuku