HausaTv:
2025-06-15@02:41:46 GMT

Iran Ta Yi Allah Wadai Da Barazanar Da Trump Ya Yi Mata

Published: 12th, February 2025 GMT

Iran ta yi kakkausar suka kan barazanar da shugaban Amurka Donald Trump ya yi na yin amfani da karfi a kan kasar, inda ta bayyana hakan a matsayin barazana da rashin da’a.

A cikin wata wasika da ya aike a wannan Talata zuwa ga shugaban Majalisar Dinkin Duniya da shugaban kwamitin sulhu na dindindin jakadan Iran a Majalisar Dinkin Duniya, Amir Saïd Iravani, ya bayyana cewa kalaman na Trump na tada hankali sun sabawa dokokin kasa da kasa da kuma kundin tsarin mulkin MDD.

Trump ya ce zai gwammace ya kulla yarjejeniya da Iran maimakon “harba mata bam fiye da kima,” a wata hira da manema labarai a ranar Asabar.

“Na fi son kulla yarjejeniya da ba za ta cutar da su ba,” in ji shi. “Zan so in yi yarjejeniya da su ba tare da kai musu harin bam ba,” in ji Trump ga jaridar New York Post.

Iravani ya bayyana cewa, kalaman na Trump masu hadari da tayar da hankali sun sabawa dokokin kasa da kasa da kuma Yarjejeniya ta Majalisar Dinkin Duniya, musamman a shafi na 2 (4), wanda ya haramta barazana ko amfani da karfi kan kasashe masu cin gashin kai. »

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Ta Harba Tauraron Dan Adam Na Lura Da Yanayin Bala’u

A yau Asabar ne kasar Sin ta yi nasarar harba tauraron dan Adam na lura da yanayin bala’u a doron kasa, wanda ake sa ran zai rika samar da bayanai ga kasar Sin dangane da aukuwar bala’u daga indallahi, ta aikewa da sakwanni tsakanin sararin samaniya zuwa doron duniya.

An harba tauraron dan Adam din mai suna Zhangheng 1-02, ta amfani da rokar Long March-2D, daga tashar harba kumbuna ta Jiuquan dake arewa maso yammacin kasar Sin, da karfe 4 saura mintuna 4 agogon Beijing, ya kuma shiga da’irarsa ba tare da wata matsala ba, kamar dai yadda hukumar kula da binciken sararin samaniya ta kasar Sin ko CNSA ta tabbatar.

Kazalika, CNSA ta ce, wannan aiki muhimmin mataki ne da Sin ta taka, a turbar nazarin yanayin doron kasa na zahiri. An sanyawa tauraron sunan wani shahararren mai kirkire-kirkire na kasar Sin, wato marigayi Zhang Heng, wanda shi ne mutum na farko a duniya, da ya kago na’urar “seismoscope” ta hasashen aukuwar girgizar kasa, shekaru sama da 1,800 da suka gabata, kuma an samar da tauraron ne da hadin gwiwar Sin da kasar Italiya. (Saminu Alhassan)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Ta Harba Tauraron Dan Adam Na Lura Da Yanayin Bala’u
  • Muhimmanci, Tasiri Da Kuma Amfanin Jigida Ga Mata
  • Gwamnati Ta Yi Barazanar Matakai Masu Tsauri Kan Masu Fasa Bututun Mai
  • Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
  • Masana Ilimin Nukiliyar Iran Sun Yi Shahada
  • Na’im Kassim: Harin HKI Akan Iran Ba Abinda Zai Jawo Mata Sai Kaskanci
  • Gwamnan Gombe Ya Yi Allah Wadai Da Kisan Da ‘Yan Daba Suka Yi Wa Amadi Kasiran
  • Iran tana da hakkin mayar da martani ga Isra’ila : Sanarwar Ma’aikatar harkokin waje
  • Cikakken Jerin Sunaye: Tinubu Ya Karrama ‘Yan Nijeriya 102 Don Bukin Ranar Dimokuradiyya Ta 2025
  • Ranar Tattaunawa Tsakanin Wayewar Kan Kasa Da Kasa: Sabon Tunani Don Wanzar Da Zaman Lafiya Da Daidaito A Duniya