HausaTv:
2025-04-30@23:45:10 GMT

Aljeriya Ta Yi Maraba Da Shirin Iran Na Gudanar Da Taron OIC Kan Gaza

Published: 12th, February 2025 GMT

Kasar Aljeriya ta yi marhabin da shirin Iran na gudanar da taron kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta OIC a zirin Gaza, wanda shugaban na Amurka ya ce yana son karbe iko tare da raba al’ummar kasar baki daya.

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araghchi ya gabatar da shawarar gudanar da wani zama na musamman na kungiyar OIC a ranar Litinin yayin wata tattaunawa ta wayar tarho da takwaransa na kasar Aljeriya Ahmed Attaf, a wani bangare na tuntubar da yake yi da ministocin harkokin wajen kasashen musulmi kan Gaza.

A yayin tattaunawar tasa, Mista Araghchi ya yi cikakken bayani kan shawarwarin da ya yi a baya-bayan nan da shugabannin kasashen musulmi, da kuma babban sakataren kungiyar OIC, Hussein Ibrahim Taha, da Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya, Antonio Guterres, don jawo hankalin al’ummar duniya kan “makircin tsarkake kabilanci a Gaza”.

Shugaban diflomasiyyar na Iran ya yi maraba da matakin da Aljeriya ta dauka na nuna goyon baya ga tsayin daka da al’ummar Palastinu suke yi na ‘yantar da kansu daga mamayar Isra’ila.

A makon da ya gabata, Trump ya ce Amurka na neman “karbe” Gaza a wani bangare na shirin da ya gabatar a karkashin sunan “sake gina” yankin Falasdinawa da yaki ya daidaita, inda ya ba da shawarar tilastawa wasu ‘yan Gazan miliyan 2.4 gudun hijira zuwa Masar da Jordan.

Tuni dai Alkahira da Amman suka yi watsi da shirin na Trump na tunzura jama’a.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

DAGA LARABA: Asarar Da Hausawa Ke Tafkawa Sakamakon Bacewar Tatsuniya

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Tatsuniya wata hanya ce ta ilmantarwa da bayar da tarbiyya da kuma koyar da al’adu da halaye na gari a tsakanin Hausawa.

Tatsuniyoyi na ɗauke da darussa na rayuwa, suna kuma koya wa yara da manya jarumta da tausayi da sauran dabi’u kyawawa.

Sai dai a yayin da duniya take sauyawa, ba kasafai matasa suke sha’awar sauraron tatsuniya ba.

NAJERIYA A YAU: Dalilin karyewar farashin shinkafa a kasuwannin Najeriya DAGA LARABA: Dalilan Rashin Wutar Lantarki A Wasu Jihohin Arewa

Wannan ne batun da shirin Daga Laraba na wannan makon zai yi nazari a kai.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Araghchi : Za’ayi Tattaunawar Iran da Amurka ta gaba a Rome bayan taron E3
  • Xi Ya Jaddada Muhimmancin Tsara Nagartaccen Shirin Raya Tattalin Arziki Da Zamantakewar Al’umma Tsakanin 2026-2030
  • DAGA LARABA: Asarar Da Hausawa Ke Tafkawa Sakamakon Bacewar Tatsuniya
  • Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya
  • An Fara Baje Kolin Kayakin Da Ake Kerawa A Iran Tare Da Taron Iran Da Afirka Karo Na Uku
  • NAJERIYA A YAU: Dalilin karyewar farashin shinkafa a kasuwannin Najeriya
  • Shugaban Kasar Yana Maraba Da Masu Zuba Hannun Jari A Kasarsa Daga Kasashen Waje
  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Jaddada Wajabcin Komawa Kan Shirin Tsagaita Bude Wuta A Gaza
  • Tawagar Jami’ai Da ‘Yan Kasuwar Ta Tunusiya Ta Gana Da Mataimakin Shugaban kasar Iran
  • NAJERIYA A YAU: “Dalilin da muke sauya sheƙa zuwa jam’iyya mai mulki”