Gwamnati Na ɗaukar Matakai Don Rage Farashin Abinci Ta Hanyar Zuba Jari A Noma – Minista
Published: 12th, February 2025 GMT
Ya ce: “A baya, muna da wasu hukumomi da ke ƙayyade farashin kayan abinci, amma domin kasuwanci na ’yanci da bunƙasa harkokin noma, gwamnati ba ta ga dacewar ci gaba da hakan ba.
“Yanzu abin da gwamnati ke yi shi ne ta tabbatar da cewa ana samar da isassun kayan abinci, domin idan abu yana da yawa, farashin sa yana sauka da kan sa.
Ministan ya kuma bayyana nasarorin da aka samu a fannin tsaro, inda ya ce a shekarar 2024 jami’an tsaro sun kashe ’yan ta’adda da ’yan bindiga sama da 8,000, sun kama mutum 11,600, tare da ƙwato makamai fiye da 10,000.
Ya tabbatar da cewa ƙoƙarin da ake yi yana sa hanyoyi na ƙara zama lafiya.
Ya ƙara da cewa, “Ko da yake har yanzu muna da aiki a gaba, hanyoyin mu sun fara zama mafi aminci.
“Hanyar Abuja zuwa Kaduna, wadda aka fi sani da rashin tsaro, tana daga cikin misalan da ke nuna irin cigaban da muke samu.
“Kamar yadda na faɗa, har yanzu akwai aiki da yawa a gaba, kuma ba za mu yi ƙasa a gwiwa ba.
“Haka kuma, sama da mutum 8,000 da aka sace an kuɓutar da su cikin nasara.
“Za mu ci gaba da ƙoƙarin rage yawan waɗanda ake sacewa tare da bunƙasa nasarorin mu wajen hana laifuka, gano masu ma’aikatan su, da kuma hukunta su.”
Idris ya ƙara da cewa, bayan da Kotun Tarayya ta ayyana ƙungiyar Lakurawa a matsayin ’yan ta’adda, jami’an tsaro sun samu cikakken ikon amfani da ƙarfin da ya dace wajen murƙushe su.
Dangane da tattalin arziki, Ministan ya bayyana cewa sauye-sauyen da gwamnati ke aiwatarwa suna samar da ingantaccen sakamako, musamman cire tallafin fetur wanda ya hana asarar ɗaruruwan biliyoyin naira a kowace shekara.”
Ya jaddada cewa shigar da tsarin Electronic Foreign Exchange Matching System (EFEMS) a watan Disamba na 2023 ya inganta gaskiya a harkar canjin kuɗi, inda ya taimaka wajen warware bashin dalar Amurka da aka tara tun baya, da kuma dawo da ƙwarin gwiwar masu zuba jari.
“Makon jiya, Naira ta kai matsayi mafi ƙarfi cikin watanni takwas a kasuwar canji ta hukuma, yayin da jarin da ƙasashen waje ke zubawa a Kasuwar Hannun Jari ta Nijeriya ya ƙaru daga kashi 4 a tsakiyar 2023 zuwa kashi 16 a ƙarshen 2024.”
Ministan ya kuma bayyana cewa a shekarar 2024, Nijeriya ta zama ƙasa mafi jan hankalin masu zuba jari a ɓangaren man fetur da iskar gas a nahiyar Afrika, inda aka samu sama da dala biliyan 5.
Idris ya bayyana shekarar 2025 a matsayin shekara ta cigaba da gina nasarorin da aka samu a cikin wa’adin farko na mulkin Tinubu.
Ya ce za a gudanar da tarukan ministoci a duk mako na tsawon watanni uku masu zuwa domin tattauna nasarorin da aka samu a fannoni daban-daban.
Ya ce: “A cikin watanni uku masu zuwa, yayin da muke gab da cika shekaru biyu na mulkin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, za mu kawo ministoci zuwa wannan dandali a kowanne mako.
“Shekarar 2025 ita ce shekara ta ƙarfafa nasarorin da muka samu a cikin watanni 19 na farko na wannan gwamnati.
“Wannan zaman farko na 2025 dama ce ta tunatar da mu waɗannan nasarori da kuma tabbatar da irin cigaban da ake samu yayin da muke shirin shiga rabin wa’adin mulkin nan.”
কীওয়ার্ড: nasarorin da
এছাড়াও পড়ুন:
Kotu ta tsige dan majalisar da ya sauya sheka zuwa APC
Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta tsige dan majalisar wakilai, Abubakar Gummi daga kujerarsa saboda sauya sheka daga jam’iyyar PDP zuwa APC.
Gummi yana wakiltar mazabar Gummi/Bukkuyum ta Jihar Zamfara a majalisar wakilai.
An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m An sake kama shi a cikin ’yan fashi kwana 5 da fitowa daga kurkukuMai shari’a Obiora Egwuatu ne, ya yanke hukuncin, inda ya umarci kakakin majalisar wakilai, Tajudeen Abbas, da ya daina amincewa da Gummi a matsayin dan majalisar da ke wakiltar mazabar Gummi/Bukkuyum.
Haka kuma ya umarci hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) da ta shirya sabon zabe cikin kwanaki 30 domin cike gurbin kujerar dan majalisar.
Jam’iyyar PDP tare da shugaban ta na jihar Zamfara, Jamilu Jibomagayaki, ne suka shigar da karar dan majalisar.
Sun ce bai dace Gummi ya ci gaba da zama a kujerar ba bayan barin jam’iyyar da ta tsayar da shi takara.
Gummi, ta bakin lauyansa ya ce ya fice daga PDP ne saboda rikicin cikin gida da jam’iyyar ke fama da shi a matakin kasa da kuma a mazabarsa.
Amma kotu ta yi watsi da wannan hujjar, inda ta bayyana cewa babu takaddama da za ta ba shi damar ya sauya sheka.
A hukuncin da ya yanke, Mai shari’a Egwuatu ya ce ’yan siyasa dole su mutunta zabin jama’ar da suka kada musu kuri’a a karkashin jam’iyyar da ta tsayar da su takara.
Ya ce doka ba ta yadda da dan siyasa ya bar jam’iyyar da ta taimaka masa wajen lashe zabe sannan ya koma wata jam’iyya ba tare da ajiye mukaminsa ba.
Ya kara da cewa kuri’un da aka kada don dan takarar na jam’iyya ne, ba nasa ne na kashin kansa ba.
“Idan mutum yana son sauya sheka, ka da ya dauki amanar jama’ar da ta zabe shi ya tafi da ita,” in ji alkalin.
Kotu ta kuma umarci Gummi da ya daina karbar albashi da wasu hakkoki a matsayin dan majalisa, tare da mayar da duk kudaden da ya karba daga ranar 30 ga watan Oktoba, 2024, zuwa ranar da aka yanke hukuncin.
Haka kuma, ya gabatar da hujjar mayar da kudaden ga kotu cikin kwanaki 30.
Mai shari’a Egwuatu ya kuma ci Gummi tarar Naira N500,000, domin biyan PDP kudaden da ta kashe wajen shigar da kara.