Leadership News Hausa:
2025-06-15@06:30:34 GMT

Ba Za a Iya Dakile Rarrabuwar Iko Tsakanin Kasashen Duniya Ba 

Published: 12th, February 2025 GMT

Ba Za a Iya Dakile Rarrabuwar Iko Tsakanin Kasashen Duniya Ba 

Yau Talata, kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin Guo Jiakun ya gudanar da taron manema labarai da aka saba yi yau da kullum, inda ya yi tsokaci game da rahoton dake da alaka da rarrabuwar iko tsakanin kasashen duniya na taron tsaro na Munich, yana cewa, bisa binciken da taron ya yi, kasa da kasa sun kara amincewa da kasancewar iko tsakanin kasashe daban daban a duniya.

Kuma bangaren Sin ya yi imanin cewa, ba za a iya dakile wannan ci gaban da duniya ta samu ba.

Da ya tabo batun sanya na’urar Buoy da Sin ta yi cikin ruwa don duba yanayin cikin tekun da batun ya shafa, Guo Jiakun ya bayyana cewa, wannan ya dace da dokokin cikin gida na kasar Sin da kuma dokokin kasa da kasa.

Guo Jiakun ya kuma kara da cewa, kasar Sin ta kasance mai kwazo da himma wajen tunkarar sauyin yanayi, kuma za ta cika alkawarinta na cimma burin “daidaita abubuwa masu dumama yanayi da rage fitar da su” bisa hanyoyin da ta zaba. (Safiyah Ma)

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

An Samu Babban Canji Kan Tsarin Ciniki A Tsakanin Sin Da Afirka

Bisa rahoton bunkasar hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya a tsakanin Sin da nahiyar Afirka na shekarar 2025, wanda aka gabatar a jiya Juma’a 13 ga wata, an ce a halin yanzu, an samu babban sauyi a tsarin ciniki tsakanin Sin da Afirka, an kuma kyautata tsarin zuwa mai shafar fannoni da dama, mai inganci, mai kunshe da fasahohin zamani, kana a nan gaba za a samu karin damar hadin gwiwarsu a fannonin masana’antu, da aikin noma, da sadarwa, da tattalin arziki ta yanar gizo, da ayyukan more rayuwa, da makamashi mai tsafta, da hada-hadar kudi da sauransu.

A matsayin daya daga cikin manyan nasarorin da aka cimma a gun bikin baje koli na tattalin arziki da cinikayya a tsakanin Sin da Afirka karo na 4, an gabatar da rahoton ne a taron gabatar da shirye-shiryen ayyukan hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya a tsakanin Sin da Afirka, wanda aka gudanar a wannan rana.

Rahoton ya yi bayanin cewa, a shekarun baya-baya nan, an fadada cinikayyar Sin da Afirka, yawan kudin cinikayyar kaya tsakaninsu a shekarar 2023 ya zarce dalar Amurka biliyan 280, kuma yawan kudin cinikin hidimomi a tsakaninsu a shekarar 2021 ya kai sama da dalar Amurka biliyan 41 da miliyan 866, kana an kyautata tsarin cinikinsu.

A daya bangaren kuma, yawan jarin da Sin ta zubawa Afirka ya karu, wanda yawancinsu suka shafi sha’anin gine-gine. Haka zalika, an samu nasarori a fannin gina ayyukan more rayuwa, da gudanar da ayyuka a fannonin sufuri, da wutar lantarki, da sadarwa, da madatsun ruwa da sauransu, da kuma yin hadin gwiwarsu a fannonin ba da ilmi, da aikin noma, da kiwon lafiya, da samun ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba da sauransu. (Zainab Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • Sin Ta Harba Tauraron Dan Adam Na Lura Da Yanayin Bala’u
  • An Samu Babban Canji Kan Tsarin Ciniki A Tsakanin Sin Da Afirka
  • Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
  • Iran : harin da Isra’ila ta kai ‘ ayyana yaki’ ne_ Araghchi
  • Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin
  • Kamfanonin Waje Sun Ce Dole Ne Su Shiga A Dama Da Su A Cikin Kasuwar Kasar Sin
  • Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN: An Yi Kira Ga Amurka Da Ta Cimma Daidaito Da Sin Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya
  • Ranar Tattaunawa Tsakanin Wayewar Kan Kasa Da Kasa: Sabon Tunani Don Wanzar Da Zaman Lafiya Da Daidaito A Duniya
  • MDD: Adadin ‘Yan Gudun Hijira A Duniya Ya Kai Miliyan 122