Aminiya:
2025-09-18@02:17:11 GMT

Netanyahu ya bai wa Hamas wa’adin sakin Isra’ilawan da take garkuwa da su

Published: 11th, February 2025 GMT

Shugaban Isra’ila, Benjamin Netanyahu ya gargaɗi Hamas da ta yi gaggawar sakin Isra’ilawan da take tsare da su a hannunta.

Netanyahu ya ce ya bai wa ƙungiyar wa’adin zuwa ranar Asabar da ta saki Isra’ilawan da take garkuwa da su kamar yadda aka amince a yarjejeniyar tsagaita wuta da ke tsakaninsu ta tanada.

Gwamnatin Kano za ta kafa hukumar kula da masu buƙata ta musamman ‘Nijeriya ce ƙasa ta 140 mafi rashawa a Duniya’

Netanyahu ya ce ya yi ganawa ta awa huɗu da majalisar yaƙinsa inda kowa ya bayyana kaɗuwa da halin da mutane uku da Hamas ta saka ranar Asabar suka kasance.

“Dukkanin mu mun yi maraba da buƙatar shugaba Trump na sakin mutanen zuwa ranar Asabar da rana, sannan za mu yi maraba da shirin da shugaban yake da shi na makomar Gaza.

“Bisa la’akari da sanarwar da Hamas ta fitar na karya yarjejeniyar tare da ƙin sakin waɗanda ake garkuwa da su a jiya da daddare, na umarci IDF da su haɗa kan sojoji a ciki da kewayen Gaza.

“Shawarar da muka yanke a majalisar ministoci ita ce idan har Hamas ba ta dawo mana da waɗanda take garkuwa da su ba zuwa ranar Asabar, za a kawo ƙarshen yarjejeniyar kuma dakarun IDF za su koma yaƙar Hamas har zuwa lokacin da za a samu galaba a kansu,” in ji Netanyahu.

Mun dakatar da sakin fursunonin Isra’ila — Hamas

A jiya Litinin ce Hamas ta sanar da yanke shawarar jinkirta sakin fursunonin Isra’ila nan gaba har sai abin da hali ya yi.

Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwa da ƙungiyar gwagwarmaya ta Falasɗinu ta fitar tana mai cewa an ɗauki matakin ne a matsayin mayar da martani ga keta yarjejeniyar tsagaita wuta da Isra’ila ta yi.

Sanarwar da ɓangaren sojin Hamas ɗin ya fitar ta ce “fiye da mako uku, shugabacin ƙungiyar na bibiyar yadda maƙiya suka gaza cika ka’idojin yarjejeniyar da suka cimma.

“Karya wannan ƙa’ida, har da jinkirta dawowar waɗanda suka rasa muhallansu zuwa Arewacin Gaza, inda ake fakon su tare da harbin su, da harba musu bama-bamai, a yankuna daban-daban na Gaza, wanda hakan ke nuni da yadda suka gaza ƙyale ayyukan jinƙai, da sauran yarjejeniyar da suka cimma tunda farko.

“Baya ga nan, dakarun na Hamas tun farko sun mutunta wannan alƙawari da aka yi.

Saboda haka Hamas ta ce “sakin ƙarin wasu masu rajin kafa ƙasar Yahudawa a ranar Asabar, 25 ga watan 2025, sun dakatar da shi, sai nan gaba, yayin da suke jiran maƙiya, za su fara mutunta yarjejeniyar da aka cimma da aka fara aiwatarwa makonin da suka gabata.

“Muna sake jadada aniyarmu ta ci gaba da mutunta dukkan yarjejeniya da ka’idojin da aka gindaya, idan har masu mamayar suka bi su sau da ƙafa.

Wannan dai na zuwa ne a yayin da yarjejeniyar tsagaita wuta a yaƙin da Isra’ila ke yi a Gaza ta shiga kwana na 24 a yau Talata.

Rahotanni sun ce yaƙin ya kashe fiye da Falasɗinawa 48,180, inda a yanzu aka sauya alƙaluman zuwa 62,000 saboda an ayyana waɗanda suka ɓata a matsayin matattu.

Trump ya yi barazanar soke yarjejeniyar

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce zai soke yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza sannan ya bari “ko ma mai zai faru ya faru” idan ba a saki Isra’ilawa da sauran mutanen da aka yi garkuwa da su ba daga yanzu zuwa ranar Asabar.

“A ganina, idan ba a saki mutanen da aka yi garkuwa da su ba daga yanzu zuwa ranar Asabar da ƙarfe 12 na rana, zan soke yarjejeniyar sannan na bari duk abin da zai faru ya faru,” in ji Trump.

“Muna so a dawo da su. Ina magana ne a ƙashin kaina. Isra’ila tana iya ƙin amincewa da hakan, amma dai ni a ganina, ranar Asabar da ƙarfe 12 na rana, idan ba a sake su ba, za a yi babban bala’i.”

Isra’ila ce ta karya yarjejeniyar — Erdogan

Shugaban Turkiyya, Recep Tayyip Erdogan ya ce Isra’ila ta “gaza cika alƙawurran da ta ɗauka” dangane da yarjejeniyar tsagaita wutar Gaza.

Erdogan ya ƙara da cewa “dole ne mamayar Isra’ila ta zo ƙarshe. Mamayar da suke ce ƙashin bayan duk wata matsala.”

Erdogan ya kuma ce zai aike da tallafin kayan agaji zuwa Gaza, inda ya yi kira da aka kafa ƙasar Falasɗinawa mai cin gashin kanta.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Benjamin Netanyahu Isra ilawa a yarjejeniyar tsagaita wuta zuwa ranar Asabar ranar Asabar da a ranar Asabar garkuwa da su Netanyahu ya Isra ila ta

এছাড়াও পড়ুন:

Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila

Babban daraktan kamfanin dillancin labaran kasar Qatar ya bayyana cewa taron gaggawa na kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta OIC da ke tafe yana nuni da wani muhimmin sauyi na hadin kan kasashen larabawa da musulmi dangane da laifukan da ake aikatawa kan al’ummar Palastinu.

A cewar Pars Today, dukkanin idanuwa a ranakun Lahadi da Litinin (15-16 ga Satumba, 2025) za su kasance a Doha, babban birnin kasar Qatar, wanda zai karbi bakuncin taron gaggawa na shugabannin kasashen Larabawa da na Islama, don ba da amsa ga baki daya kan harin da Isra’ila ta kai kan Qatar.

Ana gudanar da wannan taron gaggawa ne a cikin yanayi na musamman na yanki da na duniya kuma ya biyo bayan harin da Isra’ila ta kai kan Qatar. Ana dai kallonsa a matsayin wani gagarumin sauyi ba wai kawai dangane da batun Falasdinu ba, har ma da sauran ci gaban siyasa a yankin.

A cikin wannan mahallin, masana da kwararru kan harkokin yada labarai na Qatar sun jaddada cewa zaluncin da Isra’ila ke yi wa Qatar ya farfado da ra’ayin kishin kasa na Larabawa tare da sake fasalin wasu muhimman batutuwan yankin.

Hadin kan Matsayin Larabawa da Musulunci

Ahmed Al-Rumaihi, Darakta-Janar na Kamfanin Dillancin Labarai na Qatar, ya ce hanyar shari’a ta kasa da kasa ita ce mafi kyawu kuma zabin da ya dace don tunkarar ci gaba da keta haddin ‘yan mamaya na (Sionist) – na farko daga cikin laifuffukan da aka rubuta da Benjamin Netanyahu, Firayim Ministan Isra’ila ya yi. Kotunan duniya, musamman kotun shari’a ta duniya, sun kafa sharuɗɗa da yawa waɗanda ke tabbatar da girman waɗannan laifuka.

Al-Rumaihi ya kara da cewa, ana ci gaba da yin Allah-wadai da wannan mugunyar ta’addancin da Isra’ila ke yi wa kasar Qatar, a duniya, kuma wannan ba wani abu ba ne, illa dai sakamakon yadda duniya ke kara wayar da kan jama’a game da keta haddin majalisar ministocin Isra’ila.

Farfado da Ra’ayin kishin Kasa

Babban editan jaridar Al-Sharq na kasar Qatar Jaber Al-Harami ya bayyana cewa, ha’incin da Isra’ila ta yi wa Qatar ya farfado da ra’ayin kishin kasa na Larabawa zuwa wani mataki da ba a taba ganin irinsa ba, wanda ke karfafa imanin cewa ba kasa daya ba ce kawai, yankin gaba daya. Al-Harami ya jaddada cewa, Isra’ila ba ta amince da wani jan layi ba, ba ta bi yarjejeniyoyin da aka kulla ko yarjejeniya ba, a maimakon haka tana aiwatar da munanan manufofin ba tare da la’akari da ka’ida ba.

A cewar Al-Harami, ta hanyar wannan wuce gona da iri Isra’ila na neman kafa sabbin sharudda da bukatu a karkashin shirin da ake kira “Isra’ila Babba”, inda ta sanya kasashen Larabawa a gaban wani zabi na wanzuwa. Don haka wajibi ne taron na Doha ya tashi daga kace-nace zuwa aiki na hakika.

Hakazalika, Nasser Al-Azba, wani lauya na kasa da kasa, ya jaddada cewa, lokaci ya yi da ya wuce yin Allah wadai da take-take, maimakon daukar matakai masu amfani da kuma daukar matakai masu inganci a kasa.

Al-Azba ya bayyana cewa, harin da Isra’ila ta kai kan Qatar a baya-bayan nan, ya nuna karara karya ce ga yarjejeniyar Vienna ta 1968, wadda ta kafa tsarin doka na kare jami’an diflomasiyya da masu shiga tsakani na kasa da kasa. A tarihi, manzanni sun kasance suna samun cikakkiyar kariya, kuma wannan ka’ida tana cikin dokokin duniya a yau.

Lauyan dokar kasa da kasa ya kara da cewa mayar da martani bai kamata ya takaita ga matakan shari’a ba, amma kuma dole ne ya hada da kulla kawance da kasashe da ba na yammacin Turai ba kamar su China, Rasha, da kasashen BRICS, yayin da a lokaci guda za a tattara ra’ayoyin jama’a na duniya don fallasa irin ta’addancin Isra’ila.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Ministan Tsaron Kasar venezuela Ya Gargadi Amurka Dangane Da Kokarin Juyin Mulki A Kasar September 16, 2025 Pezeshkian: Ya kamata kasashen musulmi su yanke alaka da gwamnatin sahyoniya September 16, 2025 Bayanin Bayan Taron Doha Ya Yi Kira Da A Kafa Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kare Kai September 15, 2025 Fira Ministan Spain: Bai Kamata A Rika Barin “Isr’ila” Tana Shiga Gasar September 15, 2025 Shugaban Kasar Iran Ya Gana Da Sarkin Kasar Qatar A Birnin Doha September 15, 2025  Dan Kasar Iran Mai Kirkira Ya Sami Kyautar Yabo A Kasar China September 15, 2025 Fizishkiyan:  Wajibi Ne Musulmi Su Hada Kai Domin Dakatar Da Laifukan HKI September 15, 2025 Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Takwarorinsa Na Qatar, Turkiyya, Pakistan Da Labanon A Doha September 15, 2025 Kwamitin Kolin Tsron Kasar Iran Ya Amince Da Yarjejeniyar Da Aka Cimma Da Hukumar IAEA September 15, 2025 Jami’in Kasar Yemen Ya Aike Da Sako Ga Mahalarta Taron Birnin Doha Na Kasar Qatar September 15, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukumar Tarayyar Turai Ta Gabatar Da Shawarar Jingine Aiki Da Yarjejeniyar KAsuwanci Da HKI
  • Hamas Ta Karyata Gwamnatin Mamayar Isra’ila Kan Shirga Karya Don Kare Muggan Manufofinta
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 
  • Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sakamakon Kisan Kiyashin ‘Yan Sahayoniyya A Gaza Ya Kusaci 65,000
  • Hamas ta bukaci kasashen musulmi da na Larabawa su dauki mataki mai tsari kan Isra’ila
  • Rabin Sojojin Isra’ila da suka ji rauni a yakin Gaza na fama da ciwon damuwa