Leadership News Hausa:
2025-04-30@22:53:53 GMT

Babu Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Tsarinmu – Gwamnan Zamfara

Published: 12th, February 2025 GMT

Babu Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Tsarinmu – Gwamnan Zamfara

“Wannan shi ne dalilin da ya sa Gwamna Dauda Lawal ya bayyana a cikin takardar yaƙin neman zabensa gabanin zaben 2023 cewa batun tsaro ne zai sa a gaba, inda ya yi alƙawarin aiwatar da matakan shawo kan lamarin.

“A halin yanzu an shaida cewa Gwamna Lawal ya cika alƙawarin.

“Gwamnatin Gwamna Dauda Lawal ta ba da fifiko kan harkokin tsaro a jihar Zamfara, kuma ta ɗauki matakin da ya dace tun farko cewa sulhu da ‘yan bindiga ba komai ba ne illa ‘je ka na yi ka’.

“A cikin hirarraki da manema labarai daban-daban, gwamnan ya sake bayyana cewa gwamnatin jihar Zamfara ba za ta yo sulhu da ‘yan bindigar da ke addabar jihar ba.

“Ya kamata a bayyana a sarari kuma a rubuce cewa matsayin Gwamna Dauda Lawal ya kasance babu cece-kuce: babu wata gwamnati da ta san ciwon kanta da za ta yi sulhu da masu kisa.

“Tattaunawar da Gwamna Lawal ya yi da BBC Hausa ya nuna cewa matsayinsa ƙarara yake ba tare da boye-boye ba. Ya ci gaba da cewa, tun da farko idan aka samu damar sulhu, to dole ne ‘yan bindigar su miƙa wuya su tuba tare da ajiye makamansu ba tare da wani sharaɗi ko buƙata ba.

“Dabarun da muke aiwatarwa na yaƙar ‘yan bindiga na samar da sakamako mai kyau, saboda yawancin yankunan jihar da ke fama da rikici na samun dawowar zaman lafiya. Abin da ake ƙara samu a Zamfara shi ne irin nasarorin kawar da shugabannin da ɗaruruwan ’yan bindiga a kullum.”

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Rashin tsaro: Gwamnan AbdulRahman Ya Gana Da Sarakuna Masu Daraja Ta Daya A Jihar Kwara 

“Gwamnati ta amince da hada hannu da shugabannin al’umma na cikin gida domin tabbatar da tsaro.

 

“Muna gode muku kan abin da kuke yi. Amma muna bukatar Sarakuna su yi magana da mutanenmu kan kokarin da dukkanmu muke yi don kare al’ummominmu daga masu kutse.”

 

Gwamnan ya yi kira da a inganta hadin gwiwa a tsakanin al’umma da hukumomin tsaro domin kare rayuka da dukiyoyi.

 

Mataimakin Shugaban Majalisar Sarakunan Jihar Kwara, Alhaji Ibrahim Bologi II, wanda shi ne Etsu Patigi, ya yaba wa gwamnan bisa hada gwiwa da su domin tabbatar da tsaro a jihar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnan Sokoto Ya Amince Da Sauya Wa Manyan Sakatarori 25 Ma’aikatu A Jihar 
  • Sabbin Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci: Nan Ba Da Jimawa Ba, ‘Yan Ta’adda Za Su Ɗanɗana Kuɗarsu – COAS
  • Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga , Sun Ceto Fasinjoji 6 A Taraba
  • Wang Yi: Neman Sulhu Da Ja Da Baya Riba Ne Ga Masu Son Cin Zali
  • Rashin tsaro: Gwamnan AbdulRahman Ya Gana Da Sarakuna Masu Daraja Ta Daya A Jihar Kwara 
  • Gwamna Namadi Ya Nada Aisha Mujaddadi Sabuwar Shugabar Hukumar InvestJigawa
  • Jihar Kebbi Ta Kammala Shirye-shiryen Aikin Hajjin 2025
  • Hajjin 2025: Gwamna Namadi Ya Nada Sarkin Kazaure Amirul Hajj
  • Akwai Ƙarin Gishiri A Yawan  Masu Sauyin Jam’iyya Zuwa APC – El-Rufai
  • Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci Ta Yaba Wa Gwamna Lawal Kan Matakan Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Zamfara