Leadership News Hausa:
2025-06-15@22:20:46 GMT

Babu Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Tsarinmu – Gwamnan Zamfara

Published: 12th, February 2025 GMT

Babu Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Tsarinmu – Gwamnan Zamfara

“Wannan shi ne dalilin da ya sa Gwamna Dauda Lawal ya bayyana a cikin takardar yaƙin neman zabensa gabanin zaben 2023 cewa batun tsaro ne zai sa a gaba, inda ya yi alƙawarin aiwatar da matakan shawo kan lamarin.

“A halin yanzu an shaida cewa Gwamna Lawal ya cika alƙawarin.

“Gwamnatin Gwamna Dauda Lawal ta ba da fifiko kan harkokin tsaro a jihar Zamfara, kuma ta ɗauki matakin da ya dace tun farko cewa sulhu da ‘yan bindiga ba komai ba ne illa ‘je ka na yi ka’.

“A cikin hirarraki da manema labarai daban-daban, gwamnan ya sake bayyana cewa gwamnatin jihar Zamfara ba za ta yo sulhu da ‘yan bindigar da ke addabar jihar ba.

“Ya kamata a bayyana a sarari kuma a rubuce cewa matsayin Gwamna Dauda Lawal ya kasance babu cece-kuce: babu wata gwamnati da ta san ciwon kanta da za ta yi sulhu da masu kisa.

“Tattaunawar da Gwamna Lawal ya yi da BBC Hausa ya nuna cewa matsayinsa ƙarara yake ba tare da boye-boye ba. Ya ci gaba da cewa, tun da farko idan aka samu damar sulhu, to dole ne ‘yan bindigar su miƙa wuya su tuba tare da ajiye makamansu ba tare da wani sharaɗi ko buƙata ba.

“Dabarun da muke aiwatarwa na yaƙar ‘yan bindiga na samar da sakamako mai kyau, saboda yawancin yankunan jihar da ke fama da rikici na samun dawowar zaman lafiya. Abin da ake ƙara samu a Zamfara shi ne irin nasarorin kawar da shugabannin da ɗaruruwan ’yan bindiga a kullum.”

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Cikin Shekaru 2, Tinubu Ya Karɓo Bashi Fiye da Shugabannin Nijeriya 3 – Obi

Ya kammala da cewa, “Gwamnatin ta yi amfani da kuɗaɗe da yawa fiye da gwamnatocin Yar’Adua, Jonathan, da Buhari jimilla, amma babu wani cigaba da aka samu.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mataimakin Gwamnan Sakkwato bai karɓi shanun tallafin layya ba — Hukumar Zakka
  • HOTUNA: Yadda aka yi sulhu da ƙasurgumin ɗan fashin daji Ado Aliero a Katsina
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 100 a Benuwe
  • Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe
  • Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • Gwamnan Kaduna ya bai wa sabon Sarkin Moro’a sandar mulki
  • Jami’in Hamas Ya Jinjinawa Iran Kan Kakkausan Martanin Da Ta Mayar Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Sudan Ta Zargi Janar Haftar Na Libiya Da Goyon Bayan ‘Yan Tawayen Kasarta Na Rapid Support Forces
  • Gwamnan Gombe Ya Yi Allah Wadai Da Kisan Da ‘Yan Daba Suka Yi Wa Amadi Kasiran
  • Cikin Shekaru 2, Tinubu Ya Karɓo Bashi Fiye da Shugabannin Nijeriya 3 – Obi