Babu Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Tsarinmu – Gwamnan Zamfara
Published: 12th, February 2025 GMT
“Wannan shi ne dalilin da ya sa Gwamna Dauda Lawal ya bayyana a cikin takardar yaƙin neman zabensa gabanin zaben 2023 cewa batun tsaro ne zai sa a gaba, inda ya yi alƙawarin aiwatar da matakan shawo kan lamarin.
“A halin yanzu an shaida cewa Gwamna Lawal ya cika alƙawarin.
“Gwamnatin Gwamna Dauda Lawal ta ba da fifiko kan harkokin tsaro a jihar Zamfara, kuma ta ɗauki matakin da ya dace tun farko cewa sulhu da ‘yan bindiga ba komai ba ne illa ‘je ka na yi ka’.
“A cikin hirarraki da manema labarai daban-daban, gwamnan ya sake bayyana cewa gwamnatin jihar Zamfara ba za ta yo sulhu da ‘yan bindigar da ke addabar jihar ba.
“Ya kamata a bayyana a sarari kuma a rubuce cewa matsayin Gwamna Dauda Lawal ya kasance babu cece-kuce: babu wata gwamnati da ta san ciwon kanta da za ta yi sulhu da masu kisa.
“Tattaunawar da Gwamna Lawal ya yi da BBC Hausa ya nuna cewa matsayinsa ƙarara yake ba tare da boye-boye ba. Ya ci gaba da cewa, tun da farko idan aka samu damar sulhu, to dole ne ‘yan bindigar su miƙa wuya su tuba tare da ajiye makamansu ba tare da wani sharaɗi ko buƙata ba.
“Dabarun da muke aiwatarwa na yaƙar ‘yan bindiga na samar da sakamako mai kyau, saboda yawancin yankunan jihar da ke fama da rikici na samun dawowar zaman lafiya. Abin da ake ƙara samu a Zamfara shi ne irin nasarorin kawar da shugabannin da ɗaruruwan ’yan bindiga a kullum.”
এছাড়াও পড়ুন:
Majalisar Kasa Na Duba yiwuwar Dawo Da Gwamnan Jihar Rivers Fabura Kafin Cikar Wa’adin Watanni Shida.
Shugaban marasa rinjaye na Majalisar Wakilai Ali Isah, ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai na Majalisar bayan wata ganawa da mai kula da jihar Ribas Sole a Abuja.
Ali Isah, ya bayyana cewa mai kula da jihar ta Ribas ya kasance a gidan a wani bangare na ziyarar da ya saba yi domin yiwa kwamitin riko da ke sa ido kan al’amuran gwamnati.
Shugaban marasa rinjaye wanda ya jagoranci taron a madadin shugaban kwamitin wanda ya zama shugaban masu rinjaye na majalisar Farfesa Julius Ihonvere, ya bayyana gamsuwa da kokarin da mai gudanarwa shi kadai yake yi na wanzar da zaman lafiya a jihar.
Ya ce mai kula da jihar ya tuntubi manyan masu ruwa da tsaki kan rikicin shugabancin jihar Ribas, shugabannin cibiyoyin addini da na gargajiya, jami’an tsaro da sauran masu ruwa da tsaki don ganin an warware matsalar cikin ruwan sanyi domin ci gaban jihar.
Sai dai jami’in da ya gabata, ya umurci mai kula da shi kadai da ya tabbatar da cewa rikicin shugabancin jihar Ribas bai shafi biyan albashin ma’aikatan gwamnati da wadanda suka yi ritaya duk wata da fansho ba kamar yadda shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu da majalisar dokokin kasar ke yin duk mai yiwuwa don tabbatar da mulkin dimokuradiyya a kasar nan.
Ali Isah, ya kuma tabbatar da cewa kwamitin wucin gadi zai ci gaba da tuntubar mai gudanarwa da bangaren zartarwa don hana tsawaita dakatarwar daga wa’adin watanni shida domin samun ci gaba.
COV: TSIBIRI