Gwamnatin Jigawa Za Ta Kara Habbaka Noman Dabino A Jihar
Published: 11th, February 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Jigawa ta kara jaddada kudurinta na yin hadin gwiwa da wani kamfanin sarrafa dabino da kayan marmari domin inganta noman dabino da alkama a jihar.
Gwamna Umar Namadi ya bada wannan tabbaci a lokacin da tawagar Babban Daraktan kamfanin, Dakta Abubakar Musa Bamai ta ziyarci shi a gidan Gwamnati dake Dutse, Babban Birnin Jihar.
Ya bayyana cewar, Gwamnatin a shirye take ta yi aiki tare da kowace kungiya da ke da niyyar tallafa wa jin daɗin al’umma da ci gaban tattalin arzikin jihar jigawa.
Malam Umar Namadi ya kara da cewar a zancen ma dai da ake yi a halin yanzu, Jihar Jigawa ta shahara wajen noman dabino kuma ita ce ta daya a noman alkama a ƙasar nan.
Kazalika, yayi nuni da cewar ana shirin amfani da fasahar zamani domin habaka harkar noma don ci gaba da riƙe wannan matsayi.
Tunda farko a jawabinsa, Babban Daraktan kamfanin, Dakta Abubakar Musa Bamai, ya bayyana cewar sun kai ziyarar ce domin tattauna hanyoyin hadin gwiwa da Gwamnatin Jihar Jigawa wajen kafa gonakin dabino da inganta noman alkama ta amfani da fasahar zamani.
Namadi, ya ce gonakin za su kunshi nau’uka hudu na dabino da za su bai wa jihar damar fara fitar da kayayyaki zuwa ƙasashen waje maimakon amfani da su a cikin gida kawai.
Usman Mohammed Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa Jihar Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
HKI Tana Amfani Yunwa A Matsayin Makamin Yaki A Kan Falasdinawa A Gaza
Wakilin falasdinawa a kutun kasa da kasa ta ICJ da ke birnin Haque na kasar Nerthelands yace HKI tana amfani da hana kayakin agaji daga ciki har da abinci shiga gaza a matsayin makami kan Falasdinawa don kashesu.
Tashar talabijib ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Ammar Hijazi jakadan kasar Faladinu a cibiyoyin MDD a kasashen Turai yana fadar haka a gaban alkalai a kotun ta ICJ a jiya litinin.
Ya ce HKI tana kisa ta sama da makamai, sannan tana kisa ta kasa da yunwa banda haka tana ci gaba da korar Falasdinawa daga yankin yamma da kogin Jordan tun fiye da watanni 3 da sua habata.
Kutun ta bude wannan zaman ne bisa bukatar MDD ta shekara ta 2024 na bincike don tabbatar da cewa HKI tana amfani yunwaa a matsayin makami a Gaza. Ammar Hijazi ya kara da cewa banda wannan babban kotun HKI tana goyon bayan amfani da yunwa a matsayin makami a gaza tun fiye da watanni 2 da suka gabata.
Wasu lauyoyi daga kasashe daban–daban wadanda suka hada da Nerthlands da Afirka ta kudu duk sun yi magana sun kuma yi allawadai da HKI kan abinda take aikatawa a Gaza.