Trump Ya Yi Wa Falasdinawa Jordan Da Masar Barazana Akan Yankin Gaza
Published: 11th, February 2025 GMT
Shugaban kasar Amurka Donald Trump ya yi barazanar cewa matukar Falasdinawa ba su saki fursunonin Isra’ila ba daga nan zuwa Asabar, to za a kawo karshen tsagaita wutar yakin da aka yi, da komawa yaki.
Shugaban kasar ta Amurka ya shata wa’adin 12: 00 Na ranar Asabar a matsayin lokacin karshe na mika fursunonin.
Shugaban kasar ta Amurka wanda yake Magana da ‘yan jarida a ofis dinsa dake fadar White House, ya sake jaddada tsohuwar barazanar da ya yi tun kafin a rantsar da shi, na ce wa zai bude kofofin jahannama idan ba a mayar da fursunonin ba daga Gaza.”
Donald Trump ya kara da cewa, ya yi Magana da Benjamin Netanyahu akan wa’adin na karshe a ranar Asabar mai zuwa.
Dangane da batun fitar da Falasdinawa daga Gaza kuwa, shugaban kasar ta Amurka ya ce, ya yi imani da cewa Jordan za ta karbi Falasdinawan, tare da barazanar dakatar da taimakon da Amurka take bai wa kasar idan ba ta yi hakan ba.
Ita ma Kasar Masar ta fuskanci barazanar Amurka idan ba ta karbi Falasdinawan da Trump yake tunanin korarsu daga Gaza ba.
Shugaban kasar ta Amurka ya bayyana cewa, zai sayi yankin Gaza domin yin gine-gine na kasuwanci a ciki, lamarin da ya jawo masa mayar da martani daga sassa daban-daban na duniya.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Shugaban kasar ta Amurka
এছাড়াও পড়ুন:
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
A wata hira tare da gidan talabijin na Arise, Obi ya ce duk da cewa cire tallafin mai yana da muhimmanci, amma ya kamata a aiwatar da wannan tsari cikin tsari.
Ya ce ya amince cewa tallafin mai yana cike da ta’asa da cin hanci wanda akwai bukatar a kawo karshensa, amma ya yi suka ga hanyoyin da gwamnatin Tinubu take bi, yana bayyana su a matsayin wadanda aka yi ba bisa kwarewa ba.
Obi ya tambayi jagororin kula da kudin da aka ajiye daga cire tallafin, yana cewa, “Tun da aka ce manatallafin man fetur, ana cewa an cire ne saboda ba a so mu dunga ciyo bashi kuma kudaden za su ba da dama wajen zuba jari a muhimman ababen more rayuwa.
‘’Ina biliyoyin kudaden da aka tara? Ina aka zuba su a muhimman yankunan ci gaba? Kowa na sane da muhimman yankunan ci gaba da suka hada da ilimi, lafiya, da fitar da mutane daga talauci. Shin ko daya daga cikin wadannan abubuwan gda uku ya inganta? A’a.’’
Obi ya ce ya kamata a yi musayar farashi mai da masu ruwa da tsaki da kyau ta yadda zai rage tasirin ga matsalolin da ‘yan kasa ke ciki.
Da yake mayar da martini ga Obi, mai taimaka wa shugaban kasa kan batutuwan tsare-tsare, Daniel Bwala, ya bayyana dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP a matsayin mutum mai son kansa wanda ba ya da ilimin warware al’amuran da suka shafi tattalin arziki da shugabanci.
Bwala, a cikin wata sanarwa da ya wallafa ta shafinsa na sada zumunta na Tuwita, ya bayyana cewa ya yi mamakin yadda Obi ya yarda da manufofin tattalin arzikin Shugaba Tinubu, musamman kan cire tallafin mai da hada-hadar kudaden waje, amma ya jaddada cewa Obi sauran manyan ‘yan adawa suna neman samun iko ne kawai ko ta wani hali a wannan lokaci.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp