Jihar Bauchi Zata Tarbi Taron Karrama Sir Ahmadu Bello Karo Na 11
Published: 11th, February 2025 GMT
Gidauniyar tunawa da Sir Ahmadu Bello ta sanar da cewa za a gudanar da taron Karrama Sir Ahmadu Bello karo na 11 a ranar Asabar, 22 ga Fabrairun 2025, a Bauchi.
Wannan taron, wanda ke tunawa da rayuwa da gado na Sir Ahmadu Bello KBE, Sardaunan Sokoto da Firaministan tsohuwar Yankin Arewa, zai hada da jerin tattaunawa da ayyukan da zasu mayar da hankali wajen magance kalubalen tattalin arzikin yankin.
Taken taron na bana, “Alherin Duniya: Sauyw Albarkatun Halitta na Arewa zuwa Cigaba Mai Dorewa”, na zuwa ne a lokacin da ake fuskantar karin damuwa kan talauci da rashin aikin yi da rashin ci gaba duk da kasancewar Arewa na da yalwar albarkatun halitta.
Za a tattauna yadda yankin zai iya amfani da gonakin noma da ma’adinai da albarkatun ruwa wajen samun ci gaban tattalin arzikin da zai dore.
Wannan taron na tsawon mako guda zai hada da horo na kwarewar zamantakewa ga matasa a Jihar Bauchi da gabatar da tallafin karatu ga dalibai ‘yan asalin jihohin Arewa a makarantu na gaba da sakandire da kuma ba da kyaututtuka ga mutanen da suka cancanta a fannonin al’umma.
Tsohon Daraktan Gudanarwa na Bankin Duniya, Dr. Mansur Mukhtar OFR, zai gabatar da jawabi, yayin da His Excellency Senator George Akume, Sakataren Gwamnatin Tarayya, zai kasance matsayin baƙo na musamman.
His Excellency Alh. Muhammadu Inuwa Yahaya CON, Gwamnan Jihar Gombe ne wanda zai jagoranci taron, tare da Gwamnan Jihar Bauchi, His Excellency Sen. Bala Mohammed CON, a matsayin babban mai masaukin baki.
Ana sa ran manyan baki a wurin taron su hada da gwamnonin jihohi da ‘yan majalisar dokoki da ministoci da sauran manyan masu ruwa da tsaki, wanda ke nufin haɓaka tattaunawa mai ma’ana da dabaru masu amfani domin bude damar ci gaban tattalin arzikin Arewa.
Gidauniyar tunawa da Sir Ahmadu Bello tana ci gaba da aikinta na inganta ilimi da cigaban ɗan adam, da cigaban tattalin arziki a Arewa, a cikin girmamawa da gado na marigayi Sardauna.
Daraktan gidauniyar, Engr. Dr. Abubakar Gambo Umar, ya bayyana farin cikinsa dangane da wannan taron, yana mai jaddada muhimmancin albarkatun halitta na Arewa wajen tsara makomar yankin.
“Yankin Arewa na da yalwar albarkatun halitta da noma da ma’adinai da ruwa wanda zai iya zama babban dama don haɓaka ci gaban dake dorewa,” in ji shi.
“Amma wannan damar za a iya cimma ta ne kawai idan muka ɗauki hanyar gudanarwa ta haɗin gwiwa da cikakken tsarin kula da albarkatu, domin tabbatar da cewa ci gaban yana faɗaɗa ga dukkanin masu ruwa da tsaki,” ya ƙara da cewa.
Dr. Umar ya kuma bayyana muhimmancin taron Karrama Sir Ahmadu Bello a matsayin dandalin tattaunawa a kan waɗannan kalubale.
Ya kara da cewa, “Wannan jerin taron yana cikin muhimmancin gidauniyar tunawa da Sir Ahmadu Bello na ƙarfafa tattaunawa mai ma’ana a kan shugabanci da cigaba mai dorewa da haɓaka tattalin arziki.
Ya ce, “yana da muhimmanci mu haɗa muryoyi daban-daban daga gwamnati da ɓangarori masu zaman kansu, da ƙungiyoyin farar hula don ƙirƙirar dabaru masu amfani wajen ci gaban yankin.”
Khadija Kubau
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jihar Bauchi Zata Tarbi Taron Karo Karrama
এছাড়াও পড়ুন:
Rawar da Arewa za ta taka a Zaɓen 2027
’Yan siyasar yankin Arewa na ganin dole sai da goyon bayansu ɗan takara zai yi nasara a zaben Shugaban ƙasa.
Hakan na zuwa ne bayan tsohon maitaimaka wa shugaban ƙasa a fannin siyasa, Alhaji Hakeem Baba-Ahmed ya yi wata hira, inda yake cewa, nan da wata shida yankin zai fitar da matsayarsa.
An ɗaure ’yar shekara 80 a kurkuku saboda dukan jikarta da silifas Dalilin da manyan ’yan siyasa ke barin NNPP — APCDuk da cewa Hakeem ba shi ne mai magana da yawun al’ummar yankin ba, amma ana kallon sa a matsayin daya daga cikin manya a yankin, saboda tsohon matsayinsa na mai magana da yawun Kungiyar Dattawan Arewa (NEF).
Tsarin siyasar kasar nan ya sa dole ne kowane dan takara ya zaga kowane lungu da sako na kasar nan kafin ya iya samun kuri’un da yake bukata don ya samu nasara.
Masana harkokin siyasa na ganin kalaman na Hakeem da ire-irensa na kan hanya, amma idan aka cika sharadi daya kacal.
“Rawar da Arewa za ta taka a zaben 2027 ba ta da wani bambanci da wadda ta saba takawa, kuma hakan zai yiwu ne kawai idan ta ci gaba da zama dunkulalliya, mai alkibla daya,” in ji Malam Kabiru Sufi na Kwalejin Share Fagen Shiga Jami’a ta Jihar Kano.
Idan dai aka cika wannan sharaɗi, to duk wani ɗan takara ko datn Arewa ne sai ya nemi goyon bayan ‘yan Arewacin kafin ya yi nasara.
Ya bayar da misalin haɗakar da jam’iyyun siyasa suka yi kafin babban zaben 2015, inda jam’iyyun CPC da ACN da ANPP da wani ɓangare na APGA da wasu gwamnonin PDP suka kafa APC mai mulkin.
“Idan aka samu rarrabuwar kai kuma, to Arewa za ta zama kamar wani taron tsintsiya ne ba shara. Babu rawar da za ta taka”, in ji Sufi.
Malam Sufi ya ce ɗaya daga cikin dalilan da suka sa ‘yan Arewa ke jin cewa sai da su za a ci zaɓe shi ne yawan al’umma.
A zaɓen 2023 da ya gabata, sahihan kuri’un da ‘yan takara huɗun farko suka samu a jihohin Arewa sun zarta na Kudu da kusan miliyan biyar.
Bola Ahmed Tinubu na Jam’iyyar APC da Alhaji Atiku Abubakar na PDP da Mista Peter Obi na LP da Injiniya Rabi’u Musa Kwankwaso na NNPP, sun samu jimillar kuri’u miliyan 13,716,667 a jihohin Arewa. Sun samu jimillar 9,020,741 a jihohin Kudu.
Bola Tinubu da ya lashe zaɓen ya samu jimillar 5,346,404 a jihohin Arewa, yayin da ya samu 3,206,969 a jihohin Kudu.
“In dai Arewa ta sake yin abin da ta yi a 2015, tabbas dole ne sai an nemi goyon bayanta, amma idan aka samu rarrabuwar kai za ta zama mushen gizaka – ana yi mata kallon za ta iya, amma kuma ba za ta iya ba,” kamar yadda Sufi ya bayyana.
Shin ko Arewan za ta iya magana da murya ɗaya?
Farfesa Abubakar Ma’azu, masanin harkokin siyasa ne a Jami’ar Maiduguri yana ganin za ta iya yin hakan.
“Idan aka duba, wadanda suka kafa Jam’iyyar APC sun fara yunkurin ne tun a 2011.
“Abin bai yiwu ba, amma suka shiga zabe a haka kuma suka sha kaye. Sai daga baya suka gano kuskurensu kuma suka yi nasara a 2015 bayan cim ma hadakar,” in ji shi.
Ko zai yiwu a iya cin zabe da kuri’un Arewa kawai? Kamar yadda ’yan Arewa ke tutiya da cewa sai da goyon bayansu za a ci zaɓen Shugaban ƙasa, haka ma sai dan takara ya samu kuri’u a Kudanci kafin ya yi nasara.
Kafin hadakar APC ta kayar da PDP mai mulki, tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya yi takara har sau uku ba tare da nasara ba, har sai bayan da ya samu goyon bayan wasu jam’iyyu daga Kudu.
Buhari ya fara yin takara ce a Jam’iyyar APP a 2003, ya sake yi a 2007 a jam’iyyar bayan ta zama ANPP, sai a 2011 kuma ya yi a CPC.
Ana ganin shigar Jam’iyyar ACN ta Bola Tinubu cikin haɗakar APC ce ƙashin bayan nasarar Buhari, saboda yadda take da tasiri a jihohin Kudu maso Yamma da Yarabawa ke da rinjaye.
Kazalika, Atiku Abubakar na Jam’iyyar PDP a zaben 2023 ya samu kuri’u mafiya yawa a Arewaci (4,834,767) sama da kudanci (1,751,047), amma duk da haka bai yi nasara ba.
“Dole ne sai ɗan takara ya karaɗe ƙasa baki ɗaya, ya samu kuri’u a Kudu da Arewa kafin ya samu kowace irin nasara,” in ji Farfesa Ma’azu.