Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-06-15@10:32:58 GMT

Jihar Bauchi Zata Tarbi Taron Karrama Sir Ahmadu Bello Karo Na 11

Published: 11th, February 2025 GMT

Jihar Bauchi Zata Tarbi Taron Karrama Sir Ahmadu Bello Karo Na 11

 

Gidauniyar tunawa da Sir Ahmadu Bello ta sanar da cewa za a gudanar da taron Karrama Sir Ahmadu Bello karo na 11 a ranar Asabar, 22 ga Fabrairun 2025, a Bauchi.

 

 

Wannan taron, wanda ke tunawa da rayuwa da gado na Sir Ahmadu Bello KBE, Sardaunan Sokoto da Firaministan tsohuwar Yankin Arewa, zai hada da jerin tattaunawa da ayyukan da zasu mayar da hankali wajen magance kalubalen tattalin arzikin yankin.

 

 

Taken taron na bana, “Alherin Duniya: Sauyw Albarkatun Halitta na Arewa zuwa Cigaba Mai Dorewa”, na zuwa ne a lokacin da ake fuskantar karin damuwa kan talauci da rashin aikin yi da rashin ci gaba duk da kasancewar Arewa na da yalwar albarkatun halitta.

 

 

Za a tattauna yadda yankin zai iya amfani da gonakin noma da ma’adinai da albarkatun ruwa wajen samun ci gaban tattalin arzikin da zai dore.

 

 

Wannan taron na tsawon mako guda zai hada da horo na kwarewar zamantakewa ga matasa a Jihar Bauchi da gabatar da tallafin karatu ga dalibai ‘yan asalin jihohin Arewa a makarantu na gaba da sakandire da kuma ba da kyaututtuka ga mutanen da suka cancanta a fannonin al’umma.

 

 

Tsohon Daraktan Gudanarwa na Bankin Duniya, Dr. Mansur Mukhtar OFR, zai gabatar da jawabi, yayin da His Excellency Senator George Akume, Sakataren Gwamnatin Tarayya, zai kasance matsayin baƙo na musamman.

 

His Excellency Alh. Muhammadu Inuwa Yahaya CON, Gwamnan Jihar Gombe ne wanda zai jagoranci taron, tare da Gwamnan Jihar Bauchi, His Excellency Sen. Bala Mohammed CON, a matsayin babban mai masaukin baki.

 

 

Ana sa ran manyan baki a wurin taron su hada da gwamnonin jihohi da ‘yan majalisar dokoki da ministoci da sauran manyan masu ruwa da tsaki, wanda ke nufin haɓaka tattaunawa mai ma’ana da dabaru masu amfani domin bude damar ci gaban tattalin arzikin Arewa.

 

Gidauniyar tunawa da Sir Ahmadu Bello tana ci gaba da aikinta na inganta ilimi da cigaban ɗan adam, da cigaban tattalin arziki a Arewa, a cikin girmamawa da gado na marigayi Sardauna.

 

Daraktan gidauniyar, Engr. Dr. Abubakar Gambo Umar, ya bayyana farin cikinsa dangane da wannan taron, yana mai jaddada muhimmancin albarkatun halitta na Arewa wajen tsara makomar yankin.

 

“Yankin Arewa na da yalwar albarkatun halitta da noma da ma’adinai da ruwa wanda zai iya zama babban dama don haɓaka ci gaban dake dorewa,” in ji shi.

 

“Amma wannan damar za a iya cimma ta ne kawai idan muka ɗauki hanyar gudanarwa ta haɗin gwiwa da cikakken tsarin kula da albarkatu, domin tabbatar da cewa ci gaban yana faɗaɗa ga dukkanin masu ruwa da tsaki,” ya ƙara da cewa.

 

Dr. Umar ya kuma bayyana muhimmancin taron Karrama Sir Ahmadu Bello a matsayin dandalin tattaunawa a kan waɗannan kalubale.

 

Ya kara da cewa, “Wannan jerin taron yana cikin muhimmancin gidauniyar tunawa da Sir Ahmadu Bello na ƙarfafa tattaunawa mai ma’ana a kan shugabanci da cigaba mai dorewa da haɓaka tattalin arziki.

 

 

Ya ce, “yana da muhimmanci mu haɗa muryoyi daban-daban daga gwamnati da ɓangarori masu zaman kansu, da ƙungiyoyin farar hula don ƙirƙirar dabaru masu amfani wajen ci gaban yankin.”

 

 

Khadija Kubau

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jihar Bauchi Zata Tarbi Taron Karo Karrama

এছাড়াও পড়ুন:

Ƴansanda Sun Kama Shahararren Ɗan Damfarar Yanar Gizo A Bauchi

Rundunar Ƴanandan Jihar Bauchi ta kama wani matashi mai suna Umar Yau, wanda aka fi sani da “Snake,” bisa zargin damfara ta yanar gizo da satar bayanan wasu mutane. An kama Yau, mai shekaru 25 daga unguwar Yelwan Makaranta a Bauchi, bayan binciken da aka fara sakamakon ƙorafi daga wata mata da ya damfara.

Fatimah Faiz Ali Bawahab, wata ’yar kasuwa ta yanar gizo, ta kai ƙorafin cewa wani ya ƙirƙiri asusun bogi a Facebook da sunanta da hotunanta don damfarar mutane. CSP Ahmed Wakil, kakakin rundunar, ya ce wanda ake zargin ya ƙirƙiri asusun “Amizeebaby Muhd” inda ya ke tallata kasuwancin ƙarya, yana karɓar kuɗi daga mutane ta asusun banki.

Gwamnatin Bauchi Ta Fara Shirin Kirkirar Sabbin Masarautu Da Sarakuna Da Gundumomi Mataimakin Firaministan Sin Ya Gana Da Ministar Kudin Birtaniya

An gano cewa an taɓa damfarar wani Nafiu Muhd a watan Maris 2022, inda ya tura kudi zuwa asusun da ke dauke da suna Hansatu Yau, bayan haka aka toshe shi. Daga baya, bincike ya gano cewa ana amfani da sunayen Hansatu Yau da Umar Yau wajen karbar kuɗin jama’a a yanar gizo.

Bayan ƙorafin da aka samu, Kwamishinan ’Yansanda ya umurci gudanar da bincike na fasaha wanda ya kai ga kama Yau a ranar 5 ga Yuni, 2025. An kwato kati tara na ATM, katin zabe, na’urar MiFi, da sauran kayayyakin da suka tabbatar da laifin. Yau ya amsa cewa ya damfari mutane kusan 40 cikin shekaru biyar. An miƙa shi zuwa Rundunar ’Yansandan Kano don ci gaba da bincike da shari’a.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci
  • Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin
  • Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai
  • Bin Hanya Daya Da Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Muhimmin Mataki Ne Na Ba Da Tabbaci Ga Huldar Ciniki Da Tattalin Arzikin Sin Da Amurka
  • Kamfanonin Waje Sun Ce Dole Ne Su Shiga A Dama Da Su A Cikin Kasuwar Kasar Sin
  • Ƴansanda Sun Kama Shahararren Ɗan Damfarar Yanar Gizo A Bauchi
  • Gwamnatin Bauchi Ta Fara Shirin Kirkirar Sabbin Masarautu Da Sarakuna Da Gundumomi
  • Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN: An Yi Kira Ga Amurka Da Ta Cimma Daidaito Da Sin Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya
  • Cikakken Jerin Sunaye: Tinubu Ya Karrama ‘Yan Nijeriya 102 Don Bukin Ranar Dimokuradiyya Ta 2025
  • Fahimtar Sabon Tunani: Raya Kimiyya Da Fasaha Da Dogaro Da Karfi Na Kashin Kai Sun Ingiza Ci Gaban Kasar Sin