Sharhin Bayan Labarai :Traump Yana Bawa Iran Zabi Nukliya Ko Yaki
Published: 11th, February 2025 GMT
Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka. Sharhin bayan labarammu zai yi magana ne dangane da barazanar shugaban kasar Amurka ga JMI “Ko ta yarda da ta zauna kan teburin tattaunawa da ita kan shirinta na makamashin nukliya ko kuma ya tura HKI ta fermata da yaki’. Wanda ni tahir amin zan karanta.
///… A wani lokaci a cikin jirgin saman fadar shugaban kasa shugaban kasar Amurka Donal Trump ya fadawa kamfanin dillancin labaran “NewYork Post’ dangane da shirin nukliyar kasar Iran, kan cewa ya fi son ya zauna da Iraniyawa su tattauna kan shirinta na makamashin nukliya, su yarda su dakatarda duk wani abu da ya shafi nukliya, amma idan sun ki tattaunawa, kuma bai da zabi in banda ta fermata da yaki.
A maganarsa dai shugaban yana son nuna diblomasiyya da kuma lallashi ne ga kasar Amurka ta amince da yarjeniya wacce zata daina mu’amala da sinadarin Uranium kwata-kwata, a sannan zata zauna lafiya da Amurka, amma kuma ra rusa diblomasiyyarsa da, kara takuarawa Iran da sabbin takunkuman tattalin arziki, da kuma baranar kara wasu takunkuman tattalin arziki, ko kuma idan duk wadannan sun kasa shawo kan iran ta zai bude wuta a kan cibiyoyin nukliyar kasar ta Iran ne.
Wannan matsayin da shugaban kasar Iran ya bayyana ba matsayi ne na diblomasiyya ba, sai dai barazana ce, na cewa JMI bata da zabi inda banda wanda Amurka ta bada, wato ko ki yarda ki tadakar da shirin na nukliya kwata-kwata!, ki daina mu’amala da makashin nukliya, ko kuma mu farmaki da yaki. Dole ne ta zama daya daga cikin zabin da Amurka ta bata.
Sai dai bayan wannan furushin na shugaba Trump. Iran ta shigar da korafin a gaban kwamitin tsaro na MDD. Inda mataimakin ministan harkokin wajen kasar kan al-amuran sharia da kuma kasa da kasa, Kazem Gharibabadi , ya bada sanarwan cewa JMI zata shigar da korafi a gaban kwamitin tsaro na MDD. Kan cewa gwamnatin Amurka ta yi barazanar fermata da yaki.
Yaze wannan barazanar ta sabawa dokokin kasa da kasa, wace ta bawa ko wace kasa yencin kai da kuma zabin abubuwan da zata yi da wadanda basa son yin.
Shugaban Trump dai ya dade yana wannan barazanar kafin ya shiga fadar white house karo na biyu, sannan wannan ba shine karon farko da yake wannan barazanar ba. Sai dai a wannan karon ya fito karara ya bayyana shi.
Kafin haka dai su jami’an gwamnatin JMI sun yi ta sabani a tsakaninsu kan ya zauna da Amurka ne don a zauna lafiya da ita ko kuma me za’a yi?.
Amma a makon da ya gabata wato a ranar larabann da ta gabata Jagoran juyin juya halin musulinci na kasar Iran Imam Sayyid Aliyul Khaminae ya fito fili ya bayyana matsayin JMI kan wannan al-amarin wanda kuma shi ne, Iran ba zata shiga tattauna da da Amurka tare da dalilai, kwarara.
Na farko shi wannan Trump din shi ne ya fidda Amurka daga yarjenioyar JCPOA tsakanin Iran da manya manyan kasashen duniya shida. Bayan tattaunawa na shekaru kimani 2. Sannan sauran suka saba wa alkawalin da suka dawkawwa Iran a JCPOA.
Wani tattanawa kuma za’a yi da shi. Bayan da takunkuman tattalin arzikinsa suna dabaibaye da kasar Iran. Don haka ya kammala da cewa mai hankali, da kuma wanda yake son mutuncinsa, har ‘iala yau wanda baya son daukar kaskasci ba zai amince da hakan ba, Don haka Iran ba zata yi tattaunawa da wani da cikin wadannan kasashen yamma ba.
Wannan ya sa dukkan mutanen kasar Iran yan siyasa da sauran mutane suka dawo kan ra’ayin jagoran.
Don haka a halin yanzu sai mu jira mu gani me Trump zai yi bayan wannan matsaya mai karfai .
Banda haka jagoram ya bayyana cewa idan Amurka ta yi barazana , zasu yi mata barazana idan ka kawowa Iramn hari zata rama.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Pezeshkian: Ya kamata kasashen musulmi su yanke alaka da gwamnatin sahyoniya tare da kiyaye hadin kai
Shugaban kasar Iran yana mai jaddada cewa wajibi ne kasashen musulmi su karfafa hadin kai da hadin kai don mayar da martani ga ayyukan gwamnatin sahyoniyawan, inda ya ce: Wajibi ne kasashen musulmi su tsaya tsayin daka tare da daukar matakai na zahiri a fagen tattalin arziki, al’adu da zamantakewa, yanke alakarsu da gwamnatin sahyoniyawan.
Masoud Pezeshkian shugaban kasar Iran a jiya litinin kafin ya tashi zuwa kasar Qatar domin halartar taron gaggawa na kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta OIC da kungiyar hadin kan kasashen larabawa dangane da harin da gwamnatin sahyoniyawan ta kai wa birnin Doha, ya bayyana cewa: “Gwamnatin yahudawan sahyoniya ba ta amince da wani iyaka ga kanta ba, kuma tare da goyon bayan Amurka, ta kai hare-hare kan kasashen musulmi da dama da suka hada da Qatar, Lebanon, Iraq, Iran, Yemen da kuma kasashen turai suna goyon bayan wadannan kasashen duniya. ayyuka.”
Shugaban na Iran ya kara da cewa: Gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila tana aiwatar da kisan kiyashi a zirin Gaza, tare da la’antar mata da yara da tsoffi, abin takaicin shi ne kasashen yammacin turai, ta hanyar goyon bayansu da kuma tanade-tanaden da suke baiwa gwamnatin wariyar launin fata ta sahyoniyawa, sun halasta wadannan ayyukan.
Pezeshkian, yayin da yake bayyana fatan sakamakon taron gaggawa na OIC da shugabannin kungiyar kasashen Larabawa, ya jaddada cewa: Dole ne kasashen musulmi su karfafa hadin kai da hadin kai don mayar da martani ga ayyukan gwamnatin sahyoniyawan da kuma kokarin tabbatar da cewa ana aiwatar da laifuffukan wannan gwamnati a dandalin kasa da kasa da na shari’a, ya kamata kasashen musulmi su tsaya tsayin daka, ta hanyar daukar matakai masu amfani a fannin tattalin arziki, al’adu, da zamantakewar al’ummar Sahayoniya.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na jaridar Pars Today cewa, a yammacin ranar Talata 9 ga watan Satumba, jiragen kasar Isra’ila sun keta sararin samaniyar kasar Qatar, inda suka yi ruwan bama-bamai a yankin Katara na birnin Doha, babban birnin kasar, inda wata babbar tawaga ta Hamas karkashin jagorancin Khalil al-Hayya ke ganawa.
A mayar da martani, an gudanar da taron ministocin harkokin wajen kungiyar OIC a jiya Lahadi a birnin Doha, wanda ya samu halartar ministan harkokin wajen kasar Iran, domin tinkarar matsalar wuce gona da iri da sojojin gwamnatin sahyoniyawan suke kaiwa kasar Qatar. Wannan taron dai ya kasance share fage ga taron kasashen musulmi da na larabawa, wanda aka shirya gudanarwa a yau litinin tare da halartar Masoud Pezeshkian shugaban jamhuriyar musulinci ta Iran.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Bayanin Bayan Taron Doha Ya Yi Kira Da A Kafa Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kare Kai September 15, 2025 Fira Ministan Spain: Bai Kamata A Rika Barin “Isr’ila” Tana Shiga Gasar September 15, 2025 Shugaban Kasar Iran Ya Gana Da Sarkin Kasar Qatar A Birnin Doha September 15, 2025 Dan Kasar Iran Mai Kirkira Ya Sami Kyautar Yabo A Kasar China September 15, 2025 Fizishkiyan: Wajibi Ne Musulmi Su Hada Kai Domin Dakatar Da Laifukan HKI September 15, 2025 Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Takwarorinsa Na Qatar, Turkiyya, Pakistan Da Labanon A Doha September 15, 2025 Kwamitin Kolin Tsron Kasar Iran Ya Amince Da Yarjejeniyar Da Aka Cimma Da Hukumar IAEA September 15, 2025 Jami’in Kasar Yemen Ya Aike Da Sako Ga Mahalarta Taron Birnin Doha Na Kasar Qatar September 15, 2025 Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sakamakon Kisan Kiyashin ‘Yan Sahayoniyya A Gaza Ya Kusaci 65,000 September 15, 2025 Gwamnatin Sudan Ta Ce: Babu Sulhu Da ‘Yan Tawayen Kasar Na Kungiyar Rapid Support Forces September 15, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci